< Genesis 17 >

1 And Abram is a son of ninety-nine years, and YHWH appears to Abram, and says to him, “I [am] God Almighty, habitually walk before Me, and be perfect;
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
2 and I give My covenant between Me and you, and multiply you very exceedingly.”
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
3 And Abram falls on his face, and God speaks with him, saying,
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
4 “I—behold, My covenant [is] with you, and you have become father of a multitude of nations;
“Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
5 and your name is no longer called Abram, but your name has been Abraham, for father of a multitude of nations have I made you;
Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
6 and I have made you exceedingly fruitful, and made you become nations, and kings go out from you.
Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
7 And I have established My covenant between Me and you, and your seed after you, throughout their generations, for a perpetual covenant, to become God to you, and to your seed after you;
zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
8 and I have given to you, and to your seed after you, the land of your sojournings, the whole land of Canaan, for a continuous possession, and I have become their God.”
Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
9 And God says to Abraham, “And you keep My covenant, you and your seed after you, throughout their generations;
Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
10 this [is] My covenant which you keep between Me and you, and your seed after you: every male of you [is] to be circumcised;
Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
11 and you have circumcised the flesh of your foreskin, and it has become a token of a covenant between Me and you.
Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
12 And a son of eight days is circumcised by you; every male throughout your generations, born in the house, or bought with money from any son of a stranger, who is not of your seed;
Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
13 he is certainly circumcised who [is] born in your house, or bought with your money; and My covenant has become in your flesh a perpetual covenant;
Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
14 and an uncircumcised one, a male, the flesh of whose foreskin is not circumcised, indeed, that person has been cut off from his people; My covenant he has broken.”
Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
15 And God says to Abraham, “Sarai your wife—you do not call her name Sarai, for Sarah [is] her name;
Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
16 and I have blessed her, and have also given to you a son from her; and I have blessed her, and she has become nations—kings of peoples are from her.”
Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
17 And Abraham falls on his face, and laughs, and says in his heart, “Is one born to the son of one hundred years? Or does Sarah—daughter of ninety years—bear?”
Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
18 And Abraham says to God, “O that Ishmael may live before You”;
Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
19 and God says, “Your wife Sarah is certainly bearing a son to you, and you have called his name Isaac, and I have established My covenant with him, for a perpetual covenant, to his seed after him.
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
20 As for Ishmael, I have heard you; behold, I have blessed him, and made him fruitful, and multiplied him, very exceedingly; twelve princes does he beget, and I have made him become a great nation;
Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
21 and My covenant I establish with Isaac, whom Sarah does bear to you at this appointed time in the next year”;
Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
22 and He finishes speaking with him, and God goes up from Abraham.
Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
23 And Abraham takes his son Ishmael, and all those born in his house, and all those bought with his money—every male among the men of Abraham’s house and circumcises the flesh of their foreskin, in this very same day, as God has spoken with him.
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24 And Abraham [is] a son of ninety-nine years in the flesh of his foreskin being circumcised;
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25 and his son Ishmael [is] a son of thirteen years in the flesh of his foreskin being circumcised;
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26 in this very same day Abraham has been circumcised, and his son Ishmael;
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27 and all the men of his house—born in the house, and bought with money from the son of a stranger—have been circumcised with him.
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.

< Genesis 17 >