< Genesis 10 >

1 And these [are] the generations of the sons of Noah, Shem, Ham, and Japheth: and sons are born to them after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Sons of Japheth [are] Gomer, and Magog, and Madai, and Javan, and Tubal, and Meshech, and Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 And sons of Gomer [are] Ashkenaz, and Riphath, and Togarmah.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 And sons of Javan [are] Elishah, and Tarshish, Kittim, and Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 By these the islands of the nations have been parted in their lands, each by his tongue, by their families, in their nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 And sons of Ham [are] Cush, and Mitzraim, and Phut, and Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 And sons of Cush [are] Seba, and Havilah, and Sabtah, and Raamah, and Sabtechah; and sons of Raamah [are] Sheba and Dedan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 And Cush has begotten Nimrod;
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 he has begun to be a hero in the land; he has been a hero in hunting before YHWH; therefore it is said, “As Nimrod the hero [in] hunting before YHWH.”
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 And the first part of his kingdom is Babel, and Erech, and Accad, and Calneh, in the land of Shinar;
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 from that land he has gone out to Asshur, and builds Nineveh, even the broad places of the city, and Calah,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 and Resen, between Nineveh and Calah; it [is] the great city.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 And Mitzraim has begotten the Ludim, and the Anamim, and the Lehabim, and the Naphtuhim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 and the Pathrusim, and the Casluhim (from where have come out Philistim), and the Caphtorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 And Canaan has begotten Sidon his firstborn, and Heth,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 and the Jebusite, and the Amorite, and the Girgashite,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 and the Hivite, and the Arkite, and the Sinite,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 and the Arvadite, and the Zemarite, and the Hamathite; and afterward the families of the Canaanite have been scattered.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 And the border of the Canaanite is from Sidon, [in] your coming toward Gerar, to Gaza; [in] your coming toward Sodom, and Gomorrah, and Admah, and Zeboim, to Lasha.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 These [are] sons of Ham, by their families, by their tongues, in their lands, in their nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 As for Shem, father of all sons of Eber, the older brother of Japheth, he has also begotten.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Sons of Shem [are] Elam, and Asshur, and Arphaxad, and Lud, and Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 And sons of Aram [are] Uz, and Hul, and Gether, and Mash.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 And Arphaxad has begotten Salah, and Salah has begotten Eber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 And two sons have been born to Eber; the name of the first [is] Peleg (for in his days the earth has been divided), and his brother’s name [is] Joktan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 And Joktan has begotten Almodad, and Sheleph, and Hazarmaveth, and Jerah,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 and Hadoram, and Uzal, and Diklah,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 and Obal, and Abimael, and Sheba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 and Ophir, and Havilah, and Jobab; all these [are] sons of Joktan;
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 and their dwelling is from Mesha, [in] your coming toward Sephar, a mountain of the east.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 These [are] sons of Shem, by their families, by their tongues, in their lands, by their nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 These [are] families of the sons of Noah, by their generations, in their nations, and by these the nations have been parted in the earth after the flood.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genesis 10 >