< Galatians 1 >

1 Paul, an apostle—not from men, nor through man, but through Jesus Christ, and God the Father, who raised Him out of the dead—
Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
2 and all the brothers with me, to the assemblies of Galatia:
Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
3 Grace to you and peace from God the Father and our Lord Jesus Christ,
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 who gave Himself for our sins, that He might deliver us out of the present evil age, according to the will of our God and Father, (aiōn g165)
Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn g165)
5 to whom [is] the glory through the ages of the ages. Amen. (aiōn g165)
a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
6 I wonder that you are so quickly removed from Him who called you in the grace of Christ to another good news—
Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
7 not that there is another, except there are certain who are troubling you, and wishing to pervert the good news of the Christ;
wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
8 but even if we or a messenger out of Heaven may proclaim good news to you different from what we proclaimed to you—let him be accursed!
Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
9 As we have said before, and now say again: if anyone may proclaim to you good news different from what you received—let him be accursed!
Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
10 For do I now persuade men, or God? Or do I seek to please men? For if I yet pleased men—I should not be Christ’s servant.
Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
11 And I make known to you, brothers, the good news that was proclaimed by me, that it is not according to man,
Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
12 for neither did I receive it from man, nor was I taught [it], but through a revelation of Jesus Christ,
Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
13 for you heard of my behavior once in Judaism, that I was exceedingly persecuting the Assembly of God, and destroying it,
Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
14 and I was advancing in Judaism above many equals in age in my own race, being more abundantly zealous of my fathers’ deliverances,
Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
15 and when God was well pleased—having separated me from the womb of my mother, and having called [me] through His grace—
Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
16 to reveal His Son in me, that I might proclaim Him as good news among the nations, I did not immediately confer with flesh and blood,
yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
17 nor did I go up to Jerusalem to those who were apostles before me, but I went away to Arabia, and again returned to Damascus;
Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
18 then, after three years I went up to Jerusalem to inquire about Peter, and remained with him fifteen days,
Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
19 and I did not see [any] other of the apostles, except James, the brother of the LORD.
Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
20 And the things that I write to you, behold, before God—I do not lie;
Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
21 then I came into the regions of Syria and of Cilicia,
Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
22 and was unknown by face to the assemblies of Judea, that [are] in Christ,
Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
23 and they were only hearing that “he who is persecuting us then, now proclaims good news—the faith that he was then destroying”;
Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
24 and they were glorifying God in me.
Sai suka yabi Allah saboda ni.

< Galatians 1 >