< Ezekiel 8 >

1 And it comes to pass, in the sixth year, in the sixth [month], on the fifth of the month, I am sitting in my house, and [the] elderly of Judah are sitting before me, and there a hand of Lord YHWH falls on me,
A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
2 and I look, and behold, a likeness as the appearance of fire, from the appearance of His loins and downward—fire, and from His loins and upward, as the appearance of brightness, as the color of electrum.
Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
3 And He puts forth a form of a hand, and takes me by a lock of my head, and [the] Spirit lifts me up between the earth and the heavens, and brings me to Jerusalem in visions of God, to the opening of the inner gate that is facing the north, where the seat of the figure of jealousy [is] that is making jealous,
Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
4 and behold, there the glory of the God of Israel [is] as the appearance that I saw in the valley.
A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
5 And He says to me, “Son of man, now lift up your eyes [toward] the way of the north.” And I lift up my eyes [toward] the way of the north, and behold, on the north of the gate of the altar [is] this figure of jealousy, at the entrance.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
6 And He says to me, “Son of man, are you seeing what they are doing? The great abominations that the house of Israel is doing here, to keep far off from My sanctuary; and turn again, [and] see great abominations.”
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
7 And He brings me to an opening of the court, and I look, and behold, a hole in the wall;
Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
8 and He says to me, “Son of man, now dig through the wall”; and I dig through the wall, and behold, an opening.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
9 And He says to me, “Go in, and see the evil abominations that they are doing here.”
Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
10 And I go in, and look, and behold, every form of creeping thing, and detestable beast—and all the idols of the house of Israel—carved on the wall, all around,
Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
11 and seventy men from [the] elderly of the house of Israel—and Jaazaniah son of Shaphan standing in their midst—are standing before them, and each [with] his censer in his hand, and [the] abundance of [the] cloud of the incense is going up.
A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
12 And He says to me, “Have you seen, son of man, that which elderly of the house of Israel are doing in the darkness, each in [the] inner chambers of his imagery, for they are saying, YHWH is not seeing us, YHWH has forsaken the land?”
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
13 And He says to me, “Turn again, [and] see [the] great abominations that they are doing.”
Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
14 And He brings me to the opening of the gate of the house of YHWH that [is] at the north, and behold, there the women are sitting, weeping for Tammuz.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
15 And He says to me, “Have you seen, son of man? Turn again, [and] see greater abominations than these.”
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
16 And He brings me into the inner court of the house of YHWH, and behold, at the opening of the temple of YHWH, between the porch and the altar, about twenty-five men, their backs toward the temple of YHWH, and their faces eastward, and they are bowing themselves eastward to the sun.
Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
17 And He says to me, “Have you seen, son of man? Has it been a light thing to the house of Judah to do the abomination that they have done here, that they have filled the land with violence, and turn back to provoke Me to anger? And behold, they are putting forth the branch to their nose!
Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
18 And I also deal in fury, My eye does not pity, nor do I spare, and they have cried [with] a loud voice in My ears and I do not hear them.”
Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”

< Ezekiel 8 >