< Ezekiel 37 >
1 There has been a hand of YHWH on me, and He takes me forth in [the] Spirit of YHWH, and places me in the midst of the valley, and it is full of bones,
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 and He causes me to pass over by them, all around, and behold, very many [are] on the face of the valley, and behold—very dry.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 And He says to me, “Son of man, do these bones live?” And I say, “O Lord YHWH, You have known.”
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 And He says to me, “Prophesy concerning these bones, and you have said to them, O dry bones, hear a word of YHWH!
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Thus said Lord YHWH to these bones: Behold, I am bringing a spirit into you, and you have lived,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 and I have given sinews on you, and cause flesh to come up on you, and covered you over with skin, and given a spirit in you, and you have lived, and you have known that I [am] YHWH.”
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 And I have prophesied as I have been commanded, and there is a noise as I am prophesying, and behold, a rushing, and the bones draw near, bone to its bone.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 And I beheld, and behold, sinews [are] on them, and flesh has come up, and skin covers them over above—and there is no spirit in them.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 And He says to me: “Prophesy to the Spirit, prophesy, son of man, and you have said to the Spirit, Thus said Lord YHWH: Come in from the four winds, O Spirit, and breathe on these slain, and they live.”
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 And I have prophesied as He commanded me, and the Spirit comes into them, and they live, and stand on their feet—a very, very great force.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 And He says to me, “Son of man, these bones are the whole house of Israel; behold, they are saying, Our bones have dried up, And our hope has perished, We have been cut off by ourselves.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Therefore, prophesy, and you have said to them, Thus said Lord YHWH: Behold, I am opening your graves, And have brought you up out of your graves, O My people, And brought you into the land of Israel.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 And you have known that I [am] YHWH, In My opening your graves, And in My bringing you up out of your graves, O My people.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 And I have given My Spirit in you, and you have lived, And I have caused you to rest on your land, And you have known that I, YHWH, have spoken, and I have done [it], A declaration of YHWH.”
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 And there is a word of YHWH to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 “And you, son of man, take one stick for yourself, and write on it, For Judah, and for the sons of Israel, his companions; and take another stick, and write on it, For Joseph, the stick of Ephraim, and all the house of Israel, his companions,
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 and bring them near to one another, to you, for one stick, and they have become one in your hand.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 And when sons of your people speak to you, saying, Do you not declare to us what these [are] to you?
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 Speak to them, Thus said Lord YHWH: Behold, I am taking the stick of Joseph, that [is] in the hand of Ephraim, and the tribes of Israel his companions, and have given them to him, with the stick of Judah, and have made them become one stick, and they have been one in My hand.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 And the sticks on which you write have been in your hand before your eyes,
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 and speak to them, Thus said Lord YHWH: Behold, I am taking the sons of Israel, From among the nations to where they have gone, And have gathered them from all around, And I have brought them into their land.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 And I have made them become one nation in the land, on mountains of Israel, And one king is to them all for king, And they are no longer as two nations, Nor are they divided anymore into two kingdoms again.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Nor are they defiled anymore with their idols, And with their abominations, And with any of their transgressions, And I have saved them out of all their dwellings, In which they have sinned, And I have cleansed them, And they have been to Me for a people, And I am to them for God.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 And My servant David [is] king over them, And they all have one shepherd, And they go in My judgments, And they keep My statutes, and have done them.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 And they have dwelt on the land that I gave to My servant, to Jacob, In which your fathers have dwelt, And they have dwelt on it, they and their sons, And their son’s sons—for all time, And My servant David [is] their prince for all time.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 And I have made a covenant of peace with them, It is a perpetual covenant with them, And I have placed them, and multiplied them, And placed My sanctuary in their midst for all time.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 And My dwelling place has been over them, And I have been to them for God, And they have been to Me for a people.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 And the nations have known that I, YHWH, am sanctifying Israel, In My sanctuary being in their midst for all time!”
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”