< Ezekiel 21 >
1 And there is a word of YHWH to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, set your face toward Jerusalem, and prophesy to the holy places, and prophesy to the ground of Israel;
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
3 and you have said to the ground of Israel, Thus said YHWH: Behold, I [am] against you, And have brought out My sword from its scabbard, And have cut off righteous and wicked from you.
ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
4 Because that I have cut off righteous and wicked from you, Therefore My sword goes out from its scabbard, To all flesh, from south to north.
Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
5 And all flesh has known that I, YHWH, Have brought out My sword from its scabbard, It does not turn back anymore.
Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
6 And you, son of man, sigh with breaking of loins, indeed, sigh before their eyes with bitterness,
“Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
7 and it has come to pass, when they say to you, Why are you sighing? That you have said: Because of the report, for it is coming, And every heart has melted, And all hands have been feeble, And every spirit is weak, And all knees go [as] waters, Behold, it is coming, indeed, it has been, A declaration of Lord YHWH.”
Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
8 And there is a word of YHWH to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 “Son of man, prophesy, and you have said, Thus said YHWH: Say, A sword, a sword is sharpened, and also polished.
“Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
10 It is sharpened so as to slaughter a slaughter. It is polished so as to have brightness, Or do we rejoice? It is despising the scepter of My son [as] every tree.
wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
11 And He gives it for polishing, For laying hold of by the hand. It is sharpened—the sword—and polished, To give it into the hand of a slayer.
“‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
12 Cry and howl, son of man, For it has been among My people, It [is] among all the princes of Israel, My people have been cast to the sword. Therefore strike on your thigh,
Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
13 Because [it is] a trier, And what if it is even despising the scepter? It will not be, a declaration of Lord YHWH.
“‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
14 And you, son of man, prophesy, And strike hand on hand, And the sword is bent a third time, The sword of the wounded! It [is] the sword of the wounded—the great one, That is entering the inner chamber to them.
“Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
15 To melt the heart, and to multiply the ruins, I have set the point of a sword by all their gates. Aah! It is made for brightness, Wrapped up for slaughter.
Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
16 Take possession of the right, place yourself at the left, To where your face is appointed.
Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
17 And I also, I strike My hand on My hand, And have caused My fury to rest; I, YHWH, have spoken.”
Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
18 And there is a word of YHWH to me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
19 “And you, son of man, appoint two ways for yourself, for the coming in of the sword of the king of Babylon; they come forth from one land, both of them. And create a station; create [it] at the top of the way of the city.
“Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
20 Appoint a way for the coming of the sword, To Rabbath of the sons of Ammon, And to Judah, in fortified Jerusalem.
Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
21 For the king of Babylon has stood at the head of the way, At the top of the two ways, to use divination, He has moved lightly with the arrows, He has inquired of the teraphim, He has looked on the liver.
Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
22 The divination [for] Jerusalem has been at his right, To place battering-rams, To open the mouth with slaughter, To lift up a voice with shouting, To place battering-rams against the gates, To pour out a mound, to build a fortification.
A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
23 And it has been to them as a false divination in their eyes, Who have sworn oaths to them, But he is causing iniquity to be remembered [so they] are caught.
Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
24 Therefore, thus said Lord YHWH: Because of your causing your iniquity to be remembered, In your transgressions being revealed, For your sins being seen, in all your doings, Because of your being remembered, You are caught by the hand.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
25 And you, wounded, wicked one, Prince of Israel, whose day has come, In the time of the iniquity of the end,
“‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
26 Thus said Lord YHWH: Turn aside the turban, and carry away the crown, This—not this—make high the low, And make low the high.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
27 An overturn, overturn, overturn, I make it, Also this has not been until the coming of Him, Whose [is] the judgment, and I have given it.
Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
28 And you, son of man, prophesy, and you have said, Thus said Lord YHWH concerning the sons of Ammon, and concerning their reproach, and you have said: A sword, a sword, open for slaughter, Polished to the utmost for brightness!
“Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
29 In seeing a vain thing for you, In divining a lie for you, To put you on the necks of the wounded of the wicked, whose day has come, In the time of the iniquity of the end.
Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
30 Turn [it] back to its scabbard; I judge you In the place where you were produced, In the land of your birth.
“‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
31 And I have poured My indignation on you, I blow against you with [the] fire of My wrath, And have given you into the hand of brutish men—craftsmen of destruction.
Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
32 You are fuel for the fire, Your blood is in the midst of the land, You are not remembered, For I, YHWH, have spoken!”
Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”