< Ezekiel 17 >

1 And there is a word of YHWH to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, put forth a riddle, and use an allegory to the house of Israel,
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 and you have said, Thus said Lord YHWH: The great eagle, great-winged, long-pinioned, Full of feathers, that has diverse colors, Has come to Lebanon, And he takes the foliage of the cedar,
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 He has cropped the top of its tender twigs, And he brings it to the land of Canaan. He has placed it in a city of merchants.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 And he takes of the seed of the land, And puts it in a field of seed, He took [it] by many waters, He has set it in a conspicuous place.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 And it springs up, and becomes a spreading vine, humble of stature, To turn its thin shoots toward itself, And its roots are under it, And it becomes a vine, and makes boughs, And sends forth beautiful branches.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 And there is another great eagle, Great-winged, and abounding with feathers, And behold, this vine has bent its roots toward him, And it has sent out its thin shoots toward him, To water it from the furrows of its planting,
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 On a good field, by many waters, it is planted, to make branches, and to bear fruit, to be for a good vine.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Say, Thus said Lord YHWH: It prospers—does he not draw out its roots, And cut off its fruit, and it is withered? [In] all the leaves of its springing it withers, And not by great strength, or by numerous people, To lift it up by its roots.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 And behold, the planted thing—does it prosper? When the east wind comes against it, does it not utterly wither? On the furrows of its springing it withers.”
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 And there is a word of YHWH to me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 “Now say to the house of rebellion, Have you not known what these [are]? Say, Behold, the king of Babylon has come to Jerusalem, And he takes its king, and its princes, And brings them to himself to Babylon.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 And he takes of the seed of the kingdom, And makes a covenant with him, And brings him into an oath, And he has taken the mighty of the land,
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 That the kingdom may be humble, That it may not lift itself up, To keep his covenant—that it may stand.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 And he rebels against him, To send his messengers to Egypt, To give to him horses, and many people, Does he prosper? Does he who is doing these things escape? And has he broken covenant and escaped?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 [As] I live—a declaration of Lord YHWH, Does he not—in the place of the king who is causing him to reign, Whose oath he has despised, And whose covenant he has broken—die with him in the midst of Babylon?
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 And not with a great force, and with a numerous assembly, Does Pharaoh maintain him in battle, By pouring out a mound, and in building a fortification, To cut off many souls.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 And he despised the oath—to break covenant, And behold, he has given his hand, And all these he has done—he does not escape.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 Therefore, thus said Lord YHWH: [As] I live—My oath that he has despised, And My covenant that he has broken, Have I not put it on his head?
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 And I have spread out My snare for him, And he has been caught in My net, And I have brought him to Babylon, And judged him there [for the] trespass That he has trespassed against Me.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 And all his fugitives, with all his bands, Fall by sword, and those remaining, They are spread out to every wind, And you have known that I, YHWH, have spoken.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Thus said Lord YHWH: I have taken of the foliage of the high cedar, And I have set [it], I crop a tender one from the top of its tender shoots, And I have planted [it] on a high and lofty mountain.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 In a mountain—the high place of Israel, I plant it, And it has borne boughs, and yielded fruit, And become a good cedar, And every bird of every [kind of] wing has dwelt under it, They dwell in the shade of its thin shoots.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 And all trees of the field have known That I, YHWH, have made the high tree low, I have set the low tree on high, I have dried up the moist tree, And I have caused the dry tree to flourish, I, YHWH, have spoken, and have done [it]!”
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”

< Ezekiel 17 >