< Exodus 8 >

1 And YHWH says to Moses, “Go to Pharaoh, and you have said to him, Thus said YHWH: Send My people away, and they serve Me;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 and if you are refusing to send [them] away, behold, I am striking all your border with frogs;
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 and the River has teemed [with] frogs, and they have gone up and gone into your house, and into the inner-chamber of your bed, and on your couch, and into the house of your servants, and among your people, and into your ovens, and into your kneading-troughs;
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 indeed, on you, and on your people, and on all your servants the frogs go up.”
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 And YHWH says to Moses, “Say to Aaron, Stretch out your hand, with your rod, against the streams, against the rivers, and against the ponds, and cause the frogs to come up against the land of Egypt.”
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 And Aaron stretches out his hand against the waters of Egypt, and the frog comes up, and covers the land of Egypt;
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 and the enchanters do so with their secrets, and cause the frogs to come up against the land of Egypt.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 And Pharaoh calls for Moses and for Aaron and says, “Make supplication to YHWH, that he may turn aside the frogs from me, and from my people, and I send the people away, and they sacrifice to YHWH.”
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 And Moses says to Pharaoh, “Beautify yourself over me; when do I make supplication for you, and for your servants, and for your people, to cut off the frogs from you and from your houses—only in the River they remain?”
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 And he says, “Tomorrow.” And he says, “According to your word [it is], so that you know that there is none like our God YHWH,
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 and the frogs have turned aside from you, and from your houses, and from your servants, and from your people; only in the River they remain.”
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 And Moses—Aaron also—goes out from Pharaoh, and Moses cries to YHWH concerning the matter of the frogs which He has set on Pharaoh;
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 and YHWH does according to the word of Moses, and the frogs die out of the houses, out of the courts, and out of the fields,
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 and they heap them up together, and the land stinks.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 And Pharaoh sees that there has been a respite, and he has hardened his heart, and has not listened to them, as YHWH has spoken.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 And YHWH says to Moses, “Say to Aaron, Stretch out your rod, and strike the dust of the land, and it has become gnats in all the land of Egypt.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 And they do so, and Aaron stretches out his hand with his rod, and strikes the dust of the land, and the gnats are on man and on beast; all the dust of the land has been gnats in all the land of Egypt.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 And the enchanters do so with their secrets, to bring out the gnats, and they have not been able, and the gnats are on man and on beast;
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 and the enchanters say to Pharaoh, “It [is] the finger of God”; and the heart of Pharaoh is strong, and he has not listened to them, as YHWH has spoken.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 And YHWH says to Moses, “Rise early in the morning, and station yourself before Pharaoh, behold, he is going out to the waters, and you have said to him, Thus said YHWH: Send My people away, and they serve Me;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 for if you are not sending My people away, behold, I am sending against you, and against your servants, and against your people, and against your houses, the beetle, and the houses of the Egyptians have been full of the beetle, and also the ground on which they are.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 And I have separated in that day the land of Goshen, in which My people are staying, that the beetle is not there, so that you know that I [am] YHWH in the midst of the land,
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 and I have put a division between My people and your people; this sign is tomorrow.”
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 And YHWH does so, and the grievous beetle enters the house of Pharaoh, and the house of his servants, and in all the land of Egypt the land is corrupted from the presence of the beetle.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 And Pharaoh calls to Moses and to Aaron and says, “Go, sacrifice to your God in the land”;
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 and Moses says, “[It is] not right to do so—for us to sacrifice the abomination of the Egyptians to our God YHWH; behold, we sacrifice the abomination of the Egyptians before their eyes—and they do not stone us!
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 We go a journey of three days into the wilderness and have sacrificed to our God YHWH as He says to us.”
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 And Pharaoh says, “I send you away, and you have sacrificed to your God YHWH in the wilderness, only do not go very far off; make supplication for me”;
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 and Moses says, “Behold, I am going out from you, and have made supplication to YHWH, and tomorrow the beetle has turned aside from Pharaoh, from his servants, and from his people; only, do not let Pharaoh add to deceive in not sending the people away to sacrifice to YHWH.”
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 And Moses goes out from Pharaoh, and makes supplication to YHWH,
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 and YHWH does according to the word of Moses, and turns aside the beetle from Pharaoh, from his servants, and from his people—there has not been one left;
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 and Pharaoh also hardens his heart at this time, and has not sent the people away.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.

< Exodus 8 >