< Exodus 4 >

1 And Moses answers and says, “And if they do not give credence to me, nor listen to my voice, and say, YHWH has not appeared to you?”
Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
2 And YHWH says to him, “What [is] this in your hand?” And he says, “A rod”;
Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
3 and He says, “Cast it to the earth”; and he casts it to the earth, and it becomes a serpent—and Moses flees from its presence.
Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
4 And YHWH says to Moses, “Put forth your hand, and lay hold on the tail of it”; and he puts forth his hand, and lays hold on it, and it becomes a rod in his hand—
Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
5 “so that they believe that YHWH, God of their fathers, has appeared to you, God of Abraham, God of Isaac, and God of Jacob.”
Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
6 And YHWH says to him again, “Now put your hand into your bosom”; and he puts his hand into his bosom, and he brings it out, and behold, his hand [is] leprous as snow;
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
7 and He says, “Put your hand back into your bosom”; and he puts his hand back into his bosom, and he brings it out from his bosom, and behold, it has turned back as his flesh—
Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
8 “and it has come to pass, if they do not give credence to you, and do not listen to the voice of the first sign, that they have given credence to the voice of the latter sign.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
9 And it has come to pass, if they do not give credence even to these two signs, nor listen to your voice, that you have taken of the waters of the River, and have poured [it] on the dry land, and the waters which you take from the River have been, indeed, they have become blood on the dry land.”
Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
10 And Moses says to YHWH, “O my Lord, I [am] not a man of words, either yesterday, or before, or since Your speaking to Your servant, for I [am] slow of mouth, and slow of tongue.”
Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
11 And YHWH says to him, “Who appointed a mouth for man? Or who appoints the mute, or deaf, or open, or blind? Is it not I, YHWH?
Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
12 And now, go, and I am with your mouth, and have directed you that which you speak”;
Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
13 and he says, “O my Lord, please send by the hand [of another that] You send.”
Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
14 And the anger of YHWH burns against Moses, and He says, “Is Aaron the Levite not your brother? I have known that he speaks well, and also, behold, he is coming out to meet you; when he has seen you, then he has rejoiced in his heart,
Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
15 and you have spoken to him, and have set the words in his mouth, and I am with your mouth, and with his mouth, and have directed you that which you do;
Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
16 and he, he has spoken to the people for you, and it has come to pass, he is to you for a mouth, and you are to him for God;
Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
17 and you take this rod in your hand, with which you do the signs.”
Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
18 And Moses goes and turns back to his father-in-law Jethro, and says to him, “Please let me go, and I return to my brothers who [are] in Egypt, and I see whether they are yet alive.” And Jethro says to Moses, “Go in peace.”
Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
19 And YHWH says to Moses in Midian, “Go, return to Egypt, for all the men who seek your life have died”;
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
20 and Moses takes his wife, and his sons, and causes them to ride on the donkey, and turns back to the land of Egypt, and Moses takes the rod of God in his hand.
Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
21 And YHWH says to Moses, “In your going to return to Egypt, see—all the wonders which I have put in your hand—that you have done them before Pharaoh, and I strengthen his heart, and he does not send the people away;
Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
22 and you have said to Pharaoh, Thus said YHWH: My son, My firstborn [is] Israel,
Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
23 and I say to you, send My son away, and he serves Me; and [if] you refuse to send him away, behold, I am slaying your son, your firstborn.”
na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
24 And it comes to pass in the way, in a lodging place, that YHWH meets him, and seeks to put him to death;
Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
25 and Zipporah takes a flint, and cuts off the foreskin of her son, and causes [it] to touch his feet, and says, “You [are] surely a bridegroom of blood to me”;
Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
26 and He desists from him. Then she said, “A bridegroom of blood,” in reference to the circumcision.
Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
27 And YHWH says to Aaron, “Go into the wilderness to meet Moses”; and he goes, and meets him on the mountain of God, and kisses him,
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
28 and Moses declares to Aaron all the words of YHWH with which He has sent him, and all the signs with which He has charged him.
Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
29 And Moses goes—Aaron also—and they gather all the elderly of the sons of Israel,
Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
30 and Aaron speaks all the words which YHWH has spoken to Moses, and does the signs before the eyes of the people;
sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
31 and the people believe when they hear that YHWH has looked after the sons of Israel, and that He has seen their affliction; and they bow and pay respect.
sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.

< Exodus 4 >