< Exodus 31 >
1 And YHWH speaks to Moses, saying,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “See, I have called by name Bezaleel, son of Uri, son of Hur, of the tribe of Judah,
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 and I fill him [with] the Spirit of God, in wisdom, and in understanding, and in knowledge, and in all work,
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 to devise inventions to work in gold, and in silver, and in bronze,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 and in a carving of stone for settings, and in a carving of wood to work in all work.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 And I, behold, have given with him Aholiab, son of Ahisamach, of the tribe of Dan, and I have given wisdom in the heart of every wise-hearted one, and they have made all that which I have commanded you.
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 The Tent of Meeting, and the Ark of Testimony, and the propitiatory covering which [is] on it, and all the vessels of the tent,
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 and the table and its vessels, and the pure lampstand and all its vessels, and the altar of the incense,
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 and the altar of the burnt-offering and all its vessels, and the laver and its base,
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 and the colored garments, and the holy garments for Aaron the priest, and the garments of his sons, for acting as priests in;
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 and the anointing oil, and the incense of the spices for the holy place; according to all that I have commanded you—they do.”
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 And YHWH speaks to Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 “And you, speak to the sons of Israel, saying, Surely you keep My Sabbaths, for it [is] a sign between Me and you throughout your generations, to know that I, YHWH, am sanctifying you;
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 and you have kept the Sabbath, for it [is] holy to you, he who is defiling it is certainly put to death—for any who does work in it—that person has even been cut off from the midst of his people.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 [For] six days work is done, and in the seventh day [is] a Sabbath of holy rest to YHWH; any who does work in the Sabbath day is certainly put to death,
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 and the sons of Israel have observed the Sabbath; to keep the Sabbath throughout their generations [is] a perpetual covenant—
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 it [is] a sign between Me and the sons of Israel for all time; for [in] six days YHWH made the heavens and the earth, and in the seventh day He has ceased and is refreshed.”
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 And He gives to Moses, when He finishes speaking with him in Mount Sinai, two tablets of the Testimony, tablets of stone, written by the finger of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.