< Exodus 3 >
1 And Moses has been feeding the flock of his father-in-law Jethro, priest of Midian, and he leads the flock behind the wilderness, and comes to the mountain of God, to Horeb;
Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
2 and the Messenger of YHWH appears to him in a flame of fire, out of the midst of the bush, and he sees, and behold, the bush is burning with fire, and the bush is not consumed.
A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
3 And Moses says, “Now I turn aside and see this great appearance. Why is the bush not burned?”
Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
4 And YHWH sees that he has turned aside to see, and God calls to him out of the midst of the bush and says, “Moses! Moses!” And he says, “Here I [am].”
Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 And He says, “Do not come near here. Cast your shoes from off your feet, for the place on which you are standing is holy ground.”
Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
6 He also says, “I [am] the God of your father, God of Abraham, God of Isaac, and God of Jacob”; and Moses hides his face, for he is afraid to look toward God.
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
7 And YHWH says, “I have certainly seen the affliction of My people who [are] in Egypt, and I have heard their cry because of its exactors, for I have known its pains;
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
8 and I go down to deliver it out of the hand of the Egyptians, and to cause it to go up out of the land to a land good and broad, to a land flowing with milk and honey—to the place of the Canaanite, and the Hittite, and the Amorite, and the Perizzite, and the Hivite, and the Jebusite.
Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
9 And now, behold, the cry of the sons of Israel has come to Me, and I have also seen the oppression with which the Egyptians are oppressing them,
Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
10 and now, come, and I send you to Pharaoh; and bring out My people, the sons of Israel, from Egypt.”
To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
11 And Moses says to God, “Who [am] I, that I go to Pharaoh, and that I bring out the sons of Israel from Egypt?”
Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
12 And He says, “Because I am with you, and this [is] the sign to you that I have sent you: in your bringing out the people from Egypt—you serve God on this mountain.”
Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
13 And Moses says to God, “Behold, I am coming to the sons of Israel, and have said to them, The God of your fathers has sent me to you, and they have said to me, What [is] His Name? What do I say to them?”
Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
14 And God says to Moses, “I AM THAT WHICH I AM.” He also says, “Thus you say to the sons of Israel: I AM has sent me to you.”
Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
15 And God says again to Moses, “Thus you say to the sons of Israel: YHWH, God of your fathers, God of Abraham, God of Isaac, and God of Jacob, has sent me to you; this [is] My Name for all time, and this [is] My memorial, to generation [and] generation.
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
16 Go, and you have gathered the elderly of Israel, and have said to them: YHWH, God of your fathers, has appeared to me, God of Abraham, Isaac, and Jacob, saying, I have certainly inspected you, and that which is done to you in Egypt;
“Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
17 and I say [that] I bring you up out of the affliction of Egypt to the land of the Canaanite, and the Hittite, and the Amorite, and the Perizzite, and the Hivite, and the Jebusite, to a land flowing [with] milk and honey.
Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
18 And they have listened to your voice, and you have entered, you and [the] elderly of Israel, to the king of Egypt, and you have said to him: YHWH, God of the Hebrews, has met with us; and now, please let us go a journey of three days into the wilderness, and we sacrifice to our God YHWH.
“Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
19 And I have known that the king of Egypt does not permit you to go, unless by a strong hand,
Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
20 and I have put forth My hand, and have struck Egypt with all My wonders, which I do in its midst—and afterward he sends you away.
Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
21 And I have given the grace of this people in the eyes of the Egyptians, and it has come to pass, when you go, you do not go empty;
“Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
22 and [every] woman has asked from her neighbor, and from her who is sojourning in her house, [for] vessels of silver, and vessels of gold, and garments, and you have put [them] on your sons and on your daughters, and have spoiled the Egyptians.”
Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”