< Exodus 18 >

1 And Jethro priest of Midian, father-in-law of Moses, hears all that God has done for Moses and for His people Israel, that YHWH has brought out Israel from Egypt,
Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
2 and Jethro, father-in-law of Moses, takes Zipporah, wife of Moses, after her parting,
Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
3 and her two sons, of whom the name of one [is] Gershom, for he said, “I have been a sojourner in a strange land”;
da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
4 and the name of the other [is] Eliezer, for, “The God of my father [is] for my help, and He delivers me from the sword of Pharaoh.”
ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
5 And Jethro, father-in-law of Moses, comes, and his sons, and his wife, to Moses, to the wilderness where he is encamping—the mountain of God;
Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
6 and he says to Moses, “I, your father-in-law Jethro, am coming to you, and your wife, and her two sons with her.”
Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
7 And Moses goes out to meet his father-in-law, and bows himself, and kisses him, and they ask of one another of welfare, and come into the tent;
Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
8 and Moses recounts to his father-in-law all that YHWH has done to Pharaoh, and to the Egyptians, on account of Israel, all the travail which has found them in the way, and [how] YHWH delivers them.
Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
9 And Jethro rejoices for all the good which YHWH has done to Israel, whom He has delivered from the hand of the Egyptians;
Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
10 and Jethro says, “Blessed [is] YHWH, who has delivered you from the hand of the Egyptians, and from the hand of Pharaoh—who has delivered this people from under the hand of the Egyptians;
“Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
11 now I have known that YHWH [is] greater than all the gods, for in the thing they have acted proudly—[He is] above them!”
Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
12 And Jethro, father-in-law of Moses, takes a burnt-offering and sacrifices [it] for God; and Aaron comes in, and all [the] elderly of Israel, to eat bread with the father-in-law of Moses, before God.
Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
13 And it comes to pass on the next day, that Moses sits to judge the people, and the people stand before Moses from the morning to the evening;
Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
14 and the father-in-law of Moses sees all that he is doing for the people and says, “What [is] this thing which you are doing for the people? Why are you sitting by yourself, and all the people standing by you from morning until evening?”
Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
15 And Moses says to his father-in-law, “Because the people come to me to seek God;
Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
16 when they have a matter, it has come to me, and I have judged between a man and his neighbor, and made known the statutes of God, and His laws.”
Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
17 And the father-in-law of Moses says to him, “The thing which you are doing [is] not good;
Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
18 you surely wear away, both you, and this people which [is] with you, for the thing is too heavy for you, you are not able to do it by yourself.
Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
19 Now listen to my voice, I counsel you, and God is with you: be for the people before God, and you have brought in the things to God;
Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
20 and you have warned them [concerning] the statutes and the laws, and have made known to them the way in which they go, and the work which they do.
Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
21 And you provide out of all the people men of ability, fearing God, men of truth, hating dishonest gain, and have placed [these] over them [for] heads of thousands, heads of hundreds, heads of fifties, and heads of tens,
Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
22 and they have judged the people at all times; and it has come to pass, they bring every great matter to you, and they judge every small matter themselves; and lighten it from off yourself, and they have borne with you.
Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
23 If you do this thing, and God has commanded you, then you have been able to stand, and all this people also goes to its place in peace.”
In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
24 And Moses listens to the voice of his father-in-law, and does all that he said,
Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
25 and Moses chooses men of ability out of all Israel, and makes them chiefs over the people [for] heads of thousands, heads of hundreds, heads of fifties, and heads of tens,
Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
26 and they have judged the people at all times; they bring the hard matter to Moses, and they judge every small matter themselves.
Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
27 And Moses sends his father-in-law away, and he goes away to his own land.
Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.

< Exodus 18 >