< Esther 7 >

1 And the king comes in, and Haman, to drink with Esther the queen,
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
2 and the king says to Esther also on the second day, during the banquet of wine, “What [is] your petition, Esther, O queen? And it is given to you; and what [is] your request? To the half of the kingdom—and it is done.”
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
3 And Esther the queen answers and says, “If I have found grace in your eyes, O king, and if to the king [it be] good, let my life be given to me at my petition, and my people at my request;
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
4 for we have been sold, I and my people, to cut off, to slay, and to destroy; and if for menservants and for maidservants we had been sold I had kept silent—but the adversity is not equal to the loss of the king.”
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
5 And King Ahasuerus says, indeed, he says to Esther the queen, “Who [is] he—this one? And where [is] this one whose heart has filled him to do so?”
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
6 And Esther says, “The man—adversary and enemy—[is] this wicked Haman”; and Haman has been afraid at the presence of the king and of the queen.
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
7 And the king has risen, in his fury, from the banquet of wine, to the garden of the house, and Haman has remained to seek for his life from Esther the queen, for he has seen that evil has been determined against him by the king.
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
8 And the king has turned back out of the garden of the house to the house of the banquet of wine, and Haman is falling on the couch on which Esther [is], and the king says, “Also to subdue the queen with me in the house?” The word has gone out from the mouth of the king, and the face of Haman they have covered.
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
9 And Harbonah, one of the eunuchs, says before the king, “Also behold, the tree that Haman made for Mordecai, who spoke good for the king, is standing in the house of Haman, in height fifty cubits”; and the king says, “Hang him on it.”
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
10 And they hang Haman on the tree that he had prepared for Mordecai, and the fury of the king has lain down.
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.

< Esther 7 >