< Esther 3 >

1 After these things has King Ahasuerus exalted Haman son of Hammedatha the Agagite, and lifts him up, and sets his throne above all the heads who [are] with him,
Bayan waɗannan al’amura, sai Sarki Zerzes ya girmama Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya ɗaukaka shi, ya kuma ba shi matsayi mafi girma fiye da na dukan sauran hakiman.
2 and all servants of the king, who [are] in the gate of the king, are bowing and doing homage to Haman, for so the king has commanded for him; and Mordecai does not bow nor pay respect.
Dukan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka riƙa durƙusa suna ba wa Haman girma, gama sarki ya ba da umarni a yi masa haka. Amma Mordekai bai durƙusa ya ba shi girma ba.
3 And the servants of the king, who [are] in the gate of the king, say to Mordecai, “Why [are] you transgressing the command of the king?”
Sa’an nan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka tambaye Mordekai, “Me ya sa ba ka yin biyayya da umarnin sarki?”
4 And it comes to pass, in their speaking to him, day by day, and he has not listened to them, that they declare [it] to Haman, to see whether the words of Mordecai stand, for he has declared to them that he [is] a Jew.
Kowace rana suna masa magana, amma ya ƙi yă yi. Saboda haka, suka faɗa wa Haman game da wannan don su ga ko za a jure da halin Mordekai, gama ya faɗa musu cewa shi mutumin Yahuda ne.
5 And Haman sees that Mordecai is not bowing and doing homage to him, and Haman is full of fury,
Sa’ad da Haman ya ga cewa Mordekai ba ya durƙusa ko yă girmama shi, sai ya fusata.
6 and it is contemptible in his eyes to put forth a hand on Mordecai by himself, for they have declared to him the people of Mordecai, and Haman seeks to destroy all the Jews who [are] in all the kingdom of Ahasuerus—the people of Mordecai.
Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya ga a kashe Mordekai kaɗai ba zai biya masa bukata ba. A maimakon haka, Haman ya nemi hanya a hallaka dukan mutanen Mordekai, wato, Yahudawa, a ko’ina a dukan masarautar Zerzes.
7 In the first month—it [is] the month of Nisan—in the twelfth year of King Ahasuerus, has one caused to fall Pur (that [is] the lot) before Haman, from day to day, and from month to month, [to] the twelfth, it [is] the month of Adar.
A shekara ta goma sha biyu ta Sarki Zerzes, a wata na farko, watan Nisan, sai suka jefa fur (wato, ƙuri’a) a gaban Haman don a zaɓi rana da watan da zai dace da ƙulle-ƙullen. Sai ƙuri’a ta fāɗa a kan wata na goma sha biyu, wato, watan Adar.
8 And Haman says to King Ahasuerus, “There is one people scattered and separated among the peoples, in all provinces of your kingdom, and their laws [are] diverse from all people, and the laws of the king they are not doing, and for the king it is not profitable to permit them;
Sai Haman ya ce wa Sarki Zerzes, “Akwai waɗansu mutanen da suke a warwatse, sun kuma bazu a cikin mutane cikin dukan lardunan masarautarka, waɗanda al’adunsu sun yi dabam da na dukan sauran mutane. Mutanen nan ba sa biyayya da dokokin sarki; ba zai yi wa sarki kyau a jure su ba.
9 if to the king [it be] good, let it be written to destroy them, and ten thousand talents of silver I weigh into the hands of those doing the work, to bring [it] into the treasuries of the king.”
In ya gamshi sarki, bari a yi doka, don a hallaka su, zan kuma sa talenti dubu goma na azurfa a cikin ma’ajin fada saboda mutanen da suka aikata wannan sha’ani.”
10 And the king turns aside his signet from off his hand, and gives it to Haman son of Hammedatha the Agagite, adversary of the Jews;
Saboda haka sarki ya zare zoben hatimi daga yatsarsa, ya ba wa Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban Yahudawa.
11 and the king says to Haman, “The silver is given to you, and the people, to do with it as [it is] good in your eyes.”
Sarki ya ce wa Haman, “Ka riƙe kuɗin, ka kuma yi da mutanen yadda ka ga dama.”
12 And scribes of the king are called, on the first month, on the thirteenth day of it, and it is written according to all that Haman has commanded, to lieutenants of the king, and to the governors who [are] over province and province, and to the heads of people and people, province and province, according to its writing, and people and people according to its tongue, in the name of King Ahasuerus it has been written and sealed with the signet of the king,
Sa’an nan aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku na wata na fari. Suka rubuta dukan umarnin Haman a irin rubutun kowane lardi, kuma cikin harshen kowane mutane, zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da gwamnonin larduna dabam-dabam, da kuma hakiman mutane dabam-dabam. Aka rubuta waɗannan a sunan Sarki Zerzes da kansa, aka kuma hatimce da zobensa.
13 and letters to be sent by the hand of the runners to all provinces of the king, to cut off, to slay, and to destroy all the Jews, from young even to old, infant and women, on one day, on the thirteenth of the twelfth month—it [is] the month of Adar—and to seize their spoil,
Aka aika’yan-kada-tă-kwana da saƙoni zuwa dukan lardunan sarki da umarni a hallaka, a karkashe, a kuma kawar da dukan Yahudawa, manya da ƙanana, mata da yara, a kuma washe kayayyakinsu.
14 a copy of the writing to be made law in each and every province is revealed to all the peoples, to be ready for this day.
Za a ba da kofin rubutun a matsayin doka a kowane lardi, a kuma sanar da mutanen kowace al’umma, domin su zauna da shiri don wannan rana.
15 The runners have gone forth, hurried by the word of the king, and the law has been given in Shushan the palace, and the king and Haman have sat down to drink, and the city Shushan is perplexed.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan-kada-tă-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a mazaunin masarauta da yake a Shusha. Sai Sarki da Haman suka zauna don su sha, amma birnin Shusha ya ruɗe.

< Esther 3 >