< Ephesians 4 >

1 I, the prisoner of the LORD, then call on you to walk worthily of the calling with which you were called,
A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
2 with all lowliness and meekness, with long-suffering, bearing with one another in love,
Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
3 being diligent to keep the unity of the Spirit in the bond of peace;
Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
4 one body and one Spirit, according as you were also called in one hope of your calling;
Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
5 one Lord, one faith, one immersion,
Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
6 one God and Father of all, who [is] over all, and through all, and in you all,
Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
7 and to each one of you was given grace, according to the measure of the gift of Christ,
Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
8 for this reason, it says, “Having gone up on high He led captive captivity, and gave gifts to men.”
Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
9 And that, He went up, what is it except that He also went down first into the lower parts of the earth?
(Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
10 He who went down is the same who also went up far above all the heavens, that He may fill all things—
Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
11 and He gave some [as] apostles, and some [as] prophets, and some [as] proclaimers of good news, and some [as] shepherds and teachers,
Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
12 to the perfecting of the holy ones, for a work of ministry, for a building up of the body of the Christ,
Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
13 until we may all come to the unity of faith and of the recognition of the Son of God, to a perfect man, to a measure of stature of the fullness of the Christ,
Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
14 that we may no longer be children, being tossed by waves and being carried around by every wind of the teaching, in the cunning of men, in craftiness, to the scheming of leading astray,
An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
15 and [speaking] truth in love, we may increase to Him [in] all things, who is the head—the Christ;
Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
16 from whom the whole body, being fitly joined together and united, through the supply of every joint, according to the working in the measure of each single part, the increase of the body makes for the building up of itself in love.
dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
17 This, then, I say, and I testify in the LORD: you are no longer to walk, as also the other nations walk, in the vanity of their mind,
To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
18 being darkened in the understanding, being alienated from the life of God, because of the ignorance that is in them, because of the hardness of their heart,
Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
19 who, having ceased to feel, gave themselves up to the licentiousness, for the working of all uncleanness in greediness;
Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
20 and you did not so learn the Christ,
Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
21 if [it] so be [that] you heard Him, and were taught in Him, as truth is in Jesus;
Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
22 concerning the former behavior you are to put off the old man, that is corrupt according to the desires of the deceit,
sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
23 and to be renewed in the spirit of your mind,
A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
24 and to put on the new man, which, according to God, was created in righteousness and kindness of the truth.
Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
25 For this reason, putting away the lying, each speak truth with his neighbor, because we are members of one another;
Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
26 be angry and do not sin; do not let the sun go down on your wrath,
“Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
27 neither give place to the Devil;
kada kuma ku ba wa Iblis dama.
28 whoever is stealing let him no longer steal, but rather let him labor, working the thing that is good with the hands, that he may have to impart to him having need.
Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
29 Let no corrupt word go forth out of your mouth, but what is good to the necessary building up, that it may give grace to the hearers;
Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
30 and do not make the Holy Spirit of God sorrowful, in which you were sealed to [the] day of redemption.
Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
31 Let all bitterness, and wrath, and anger, and clamor, and slander, be put away from you, with all malice,
Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
32 and become kind to one another, tender-hearted, forgiving one another, according as God also forgave you in Christ.
Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.

< Ephesians 4 >