< Deuteronomy 34 >

1 And Moses goes up from the plains of Moab to Mount Nebo, the top of Pisgah, which [is] on the front of Jericho, and YHWH shows him all the land—Gilead to Dan,
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 and all Naphtali, and the land of Ephraim, and Manasseh, and all the land of Judah to the Western Sea,
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 and the south, and the circuit of the Valley of Jericho, the city of palms, to Zoar.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 And YHWH says to him, “This [is] the land which I have sworn to Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, I give it to your seed; I have caused you to see with your eyes, but you do not pass over there.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 And Moses, servant of the Lord, dies there in the land of Moab, according to the command of YHWH;
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 and He buries him in a valley in the land of Moab, opposite Beth-Peor, and no man has known his burying place to this day.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 And Moses [is] a son of one hundred and twenty years when he dies; his eye has not become dim, nor has his moisture fled.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 And the sons of Israel lament Moses in the plains of Moab [for] thirty days; and the days of weeping [and] mourning for Moses are completed.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 And Joshua son of Nun is full of the spirit of wisdom, for Moses had laid his hands on him, and the sons of Israel listen to him, and do as YHWH commanded Moses.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 And there has not arisen a prophet in Israel like Moses anymore, whom YHWH has known face to face,
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 in reference to all the signs and the wonders which YHWH sent him to do in the land of Egypt, to Pharaoh, and to all his servants, and to all his land,
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 and in reference to all the strong hand and to all the great fear which Moses did before the eyes of all Israel.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.

< Deuteronomy 34 >