< Deuteronomy 27 >
1 And Moses and [the] elderly of Israel command the people, saying, “Keep all the command which I am commanding you today;
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 and it has been, in the day that you pass over the Jordan to the land which your God YHWH is giving to you, that you have raised up great stones for yourself, and plastered them with plaster,
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 and written on them all the words of this law in your passing over, so that you go into the land which your God YHWH is giving to you—a land flowing with milk and honey, as YHWH, God of your fathers, has spoken to you.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 And it has been, in your passing over the Jordan, you raise up these stones which I am commanding you today, in Mount Ebal, and you have plastered them with plaster,
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 and built an altar there to your God YHWH, an altar of stones; you do not wave iron over them.
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 You build the altar of your God YHWH [with] complete stones, and have caused burnt-offerings to ascend on it to your God YHWH,
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 and sacrificed peace-offerings, and eaten there, and rejoiced before your God YHWH,
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 and written on the stones all the words of this law, well engraved.”
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 And Moses speaks—the priests, the Levites, also—to all Israel, saying, “Keep silent and hear, O Israel: This day you have become a people for your God YHWH;
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 and you have listened to the voice of your God YHWH, and done His commands and His statutes which I am commanding you today.”
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 And Moses commands the people on that day, saying,
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 “These stand on Mount Gerizzim to bless the people, in your passing over the Jordan: Simeon, and Levi, and Judah, and Issachar, and Joseph, and Benjamin.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 And these stand, for the reviling, on Mount Ebal: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.”
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 And the Levites have answered and said to every man of Israel [with] a loud voice:
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 “Cursed [is] the man who makes a carved and molten image, an abomination [to] YHWH, work of the hands of a craftsman, and has put [it] in a secret place.” And all the people have answered and said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 “Cursed [is] he who is making light of his father and his mother.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 “Cursed [is] he who is removing his neighbor’s border.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 “Cursed [is] he who is causing the blind to err in the way.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 “Cursed [is] he who is turning aside the judgment of fatherless, sojourner, and widow.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 “Cursed [is] he who is lying with his father’s wife, for he has uncovered his father’s skirt.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 “Cursed [is] he who is lying with any beast.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 “Cursed [is] he who is lying with his sister, daughter of his father or daughter of his mother.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 “Cursed [is] he who is lying with his mother-in-law.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 “Cursed [is] he who is striking his neighbor in secret.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 “Cursed [is] he who is taking a bribe to strike a person, innocent blood.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 “Cursed [is] he who does not establish the words of this law, to do them.” And all the people have said, “Amen.”
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”