< Daniel 12 >

1 “And at that time Michael stands up, the great head, who is standing up for the sons of your people, and there has been a time of distress, such as has not been since there has been a nation until that time, and at that time your people escape, everyone who is found written in the scroll.
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 And the multitude of those sleeping in the dust of the ground awake, some to continuous life, and some to reproaches—to continuous abhorrence.
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 And those teaching shine as the brightness of the expanse, and those justifying the multitude as stars for all time and forever.”
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 “And you, O Daniel, hide the things, and seal the scroll until the time of the end, many go to and fro, and knowledge is multiplied.”
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 “And I have looked—I, Daniel—and behold, two others are standing, one here at the edge of the flood and one there at the edge of the flood,
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 and he says to the one clothed in linen, who [is] on the waters of the flood, Until when [is] the end of these wonders?
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 And I hear the one clothed in linen, who [is] on the waters of the flood, and he lifts up his right hand and his left to the heavens, and swears by Him who is living for all time, that, After a time, times, and a half, and at the completion of the scattering of the power of the holy people, all these are finished.
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 And I have heard, and I do not understand, and I say, O my lord, what [is] the latter end of these?
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 And he says, Go, Daniel; for hidden and sealed [are] the things until the time of the end.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Purify themselves, indeed, make themselves white, indeed, many are refined: and the wicked have done wickedly, and none of the wicked understand, and those acting wisely understand;
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 and from the time of the turning aside of the continuous [sacrifice], and to the giving out of the desolating abomination, [are] one thousand, two hundred, and ninety days.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 O the blessedness of him who is waiting earnestly, and comes to the one thousand, three hundred, thirty-five days.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 And you, go on to the end, then you rest, and stand in your lot at the end of the days.”
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”

< Daniel 12 >