< Amos 4 >

1 Hear this word, you cows of Bashan, Who [are] on the mountain of Samaria, Who are oppressing the poor, Who are bruising the needy, Who are saying to their lords: “Bring in, and we drink.”
Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
2 Lord YHWH has sworn by His holiness, “Behold, days are coming on you, And He has taken you away with hooks, And your posterity with fish-hooks.
Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
3 And [by] breaches you go forth, A woman before her, And you have cast down the high place,” A declaration of YHWH.
Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
4 “Enter Beth-El, and transgress, At Gilgal multiply transgression, And bring in your sacrifices every morning, Your tithes every third year.
“Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
5 And burn a thank-offering with leaven as incense, And proclaim willing gifts, sound! For so you have loved, O sons of Israel,” A declaration of Lord YHWH.
Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 “And I also—I have given to you cleanness of teeth in all your cities, And lack of bread in all your places, And you have not turned back to Me,” A declaration of YHWH.
“Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
7 “And I also—I have withheld from you the rain, While yet three months to harvest, And I have sent rain on one city, And on another city I do not send rain, One portion is rained on, And the portion on which it does not rain withers.
“Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
8 And two or three cities have wandered, To the same city to drink water, And they are not satisfied, And you have not turned back to Me,” A declaration of YHWH.
Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
9 “I have struck you with blasting and with mildew, The abundance of your gardens and of your vineyards, And of your figs, and of your olives, The palmer-worm eats, And you have not turned back to Me,” A declaration of YHWH.
“Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
10 “I have sent among you pestilence by the way of Egypt, I have slain your choice ones by sword, With your captive horses, And I cause the stink of your camps to come up—Even into your nostrils, And you have not turned back to Me,” A declaration of YHWH.
“Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
11 “I have overturned among you, Like the overturn by God of Sodom and Gomorrah, And you are as a brand delivered from a burning, And you have not turned back to Me,” A declaration of YHWH.
“Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
12 “Therefore, thus I do to you, O Israel, at last, Because this I do to you, Prepare to meet your God, O Israel.”
“Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
13 For behold, the Former of mountains, and Creator of wind, And the Declarer to man what [is] His thought, He is making dawn obscurity, And is treading on high places of earth, YHWH, God of Hosts, [is] His Name!
Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.

< Amos 4 >