< Acts 21 >

1 And it came to pass, at our sailing, having been parted from them, having run direct, we came to Coos, and the succeeding [day] to Rhodes, and there to Patara,
Bayan muka rabu da su da ƙyar, sai muka shiga jirgin ruwa, muka miƙe zuwa Kos. Kashegari muka tafi Rods daga can kuma muka je Fatara.
2 and having found a ship passing over to Phoenicia, having gone on board, we sailed,
Sai muka sami wani jirgin ruwa da zai ƙetare zuwa Funisiya, sai muka shiga muka kama tafiya.
3 and having discovered Cyprus, and having left it on the left, we were sailing to Syria, and landed at Tyre, for there was the ship discharging the cargo.
Bayan muka hangi Saifurus muka wuce shi ta kudu, sai muka ci gaba zuwa Suriya. Muka sauka a Taya, inda jirgin ruwanmu zai sauke kayansa.
4 And having found out the disciples, we tarried there seven days, and they said to Paul, through the Spirit, not to go up to Jerusalem;
Da muka sami almajirai a can, sai muka zauna da su kwana bakwai. Ta wurin Ruhu, suka yi ƙoƙari su hana Bulus wucewa zuwa Urushalima.
5 but when it came that we completed the days, having gone forth, we went on, all bringing us on the way, with women and children, to the outside of the city, and having bowed the knees on the shore, we prayed,
Amma da lokacin tashinmu ya yi, sai muka tashi muka ci gaba da tafiyarmu. Dukan almajirai da matansu da’ya’yansu suka raka mu har bayan birni, a can kuwa a bakin teku muka durƙusa muka yi addu’a.
6 and having embraced one another, we embarked in the ship, and they returned to their own friends.
Bayan mun yi bankwana da juna, sai muka shiga jirgin ruwa, su kuwa suka koma gida.
7 And we, having finished the course, from Tyre came down to Ptolemais, and having greeted the brothers, we remained one day with them;
Muka ci gaba da tafiyarmu daga Taya muka sauka a Tolemayis, inda muka gai da’yan’uwa muka yi kwana ɗaya tare da su.
8 and on the next day Paul and his company having gone forth, we came to Caesarea, and having entered into the house of Philip the evangelist—who is of the seven—we remained with him,
Da muka tashi kashegari, sai muka isa Kaisariya muka kuma sauka a gidan Filibus mai bishara, ɗaya daga cikin Bakwai ɗin nan.
9 and this one had four daughters, virgins, prophesying.
Yana da’ya’ya huɗu’yan mata da ba su yi aure ba, waɗanda suka yi annabci.
10 And we remaining many more days, there came down a certain one from Judea, a prophet, by name Agabus,
Bayan muka yi’yan kwanaki da dama a can, sai wani annabin da ake kira Agabus ya gangaro daga Yahudiya.
11 and he having come to us, and having taken up the girdle of Paul, having also bound his own hands and feet, said, “Thus says the Holy Spirit: The man whose is this girdle—so will the Jews in Jerusalem bind, and they will deliver [him] up into the hands of nations.”
Da ya zo wurinmu, sai ya ɗauki ɗamarar Bulus, ya ɗaura hannuwansa da ƙafafunsa da ita sa’an nan ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, ‘Haka Yahudawan Urushalima za su daure mai wannan ɗamara su kuma ba da shi ga Al’ummai.’”
12 And when we heard these things, we called on [him]—both we, and those of that place—not to go up to Jerusalem,
Sa’ad da muka ji haka, sai mu da mutanen da suke can muka roƙi Bulus kada yă je Urushalima.
13 and Paul answered, “Why are you weeping, and crushing my heart? For I am ready, not only to be bound, but also to die at Jerusalem for the Name of the Lord Jesus”;
Sai Bulus ya amsa ya ce, “Don me kuke kuka kuna kuma ɓata mini zuciya? A shirye nake ba ma a daure ni kawai ba, amma har ma in mutu a Urushalima saboda sunan Ubangiji Yesu.”
14 and he not being persuaded, we were silent, saying, “The will of the LORD be done.”
Da dai ya ƙi rarrasuwa, muka yi shiru, muka ce, “Bari Ubangiji yă yi nufinsa.”
15 And after these days, having taken [our] vessels, we were going up to Jerusalem,
Bayan haka, sai muka shirya muka kuma haura zuwa Urushalima.
16 and there went also of the disciples from Caesarea with us, bringing with them him with whom we may lodge, a certain Mnason of Cyprus, an aged disciple.
Waɗansu almajirai daga Kaisariya suka raka mu suka kawo mu gidan Minason, inda za mu sauka. Shi mutumin Saifurus ne kuma ɗaya daga cikin almajirai na farko.
17 And we having come to Jerusalem, the brothers gladly received us,
Sa’ad da muka zo Urushalima,’yan’uwa suka karɓe mu da murna.
18 and on the next day Paul was going in with us to James, all the elders also came,
Kashegari Bulus da sauranmu muka tafi domin mu ga Yaƙub, dukan dattawan kuwa suna nan.
19 and having greeted them, he was expounding, one by one, each of the things God did among the nations through his ministry,
Bulus ya gaishe su ya kuma ba su rahoto dalla-dalla a kan abin da Allah ya yi a cikin Al’ummai ta wurin aikinsa.
20 and they having heard, were glorifying the LORD. They also said to him, “You see, brother, how many myriads there are of Jews who have believed, and all are zealous of the Law,
Da suka ji haka, sai suka yabi Allah. Sa’an nan suka ce wa Bulus, “Ka gani ɗan’uwa, yawan dubban Yahudawan da suka gaskata, kuma dukansu masu himma ne a wajen bin doka.
21 and they are instructed concerning you, that you teach departure from Moses to all Jews among the nations, saying not to circumcise the children, nor to walk after the customs;
An sanar da su cewa kana koya wa dukan Yahudawan da suke zama a cikin Al’ummai cewa su juye daga Musa, kana kuma faɗa musu kada su yi wa’ya’yansu kaciya ko su yi rayuwa bisa ga al’adunmu.
22 what then is it? Certainly the multitude must come together, for they will hear that you have come.
To, me za mu yi ke nan? Lalle za su ji cewa ka iso,
23 This, therefore, that we say to you, do. We have four men having a vow on themselves,
saboda haka, ka yi abin da muka faɗa maka. Akwai mutum huɗu tare da mu da suka yi alkawari.
24 having taken these, be purified with them, and be at expense with them, that they may shave the head, and all may know that the things of which they have been instructed concerning you are nothing, but you walk—yourself also—keeping the Law.
Ka ɗauki waɗannan mutane, ka tafi da su ku tsarkaka gaba ɗaya, ka kuma biya musu kome don su samu su yi aski. Ta haka kowa zai sani babu gaskiya a waɗannan rahotanni game da kai, za a kuma ga cewa kai kanka kana kiyaye dokar.
25 And concerning those of the nations who have believed, we have written, having given judgment, that they observe no such thing, except to keep themselves both from idol-sacrifices, and blood, and a strangled thing, and whoredom.”
Game da Al’ummai masu bi kuwa, mun yi musu wasiƙa a kan shawararmu cewa su guji abincin da aka miƙa wa gumaka, da jini, da naman dabbar da aka maƙure da kuma fasikanci.”
26 Then Paul, having taken the men, on the following day, having purified himself with them, was entering into the temple, announcing the fulfilment of the days of the purification, until the offering was offered for each one of them.
Kashegari, sai Bulus ya ɗauki mutanen ya kuma tsarkake kansa tare da su. Sa’an nan ya tafi haikali domin yă sanar da ranar cikar tsarkakewarsu da kuma ranar da za a ba da sadaka domin kowannensu.
27 And as the seven days were about to be fully ended, the Jews from Asia having beheld him in the temple, were stirring up all the multitude, and they laid hands on him,
Da kwana bakwai ɗin suka yi kusan cika, waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya suka ga Bulus a haikali. Sai suka zuga taron duka, suka kama shi,
28 crying out, “Men, Israelites, help! This is the man who, against the people, and the Law, and this place, is teaching all everywhere; and further, also, he brought Greeks into the temple, and has defiled this holy place”;
suna ihu suna cewa “Mutanen Isra’ila ku taimake mu! Ga mutumin da yake koya wa dukan mutane ko’ina cewa su ƙi mutanenmu da dokarmu da kuma wannan wuri. Ban da haka ma, ya kawo Hellenawa a cikin filin haikali ya ƙazantar da wurin nan mai tsarki.”
29 for they had seen before Trophimus, the Ephesian, in the city with him, whom they were supposing that Paul brought into the temple.
(Dā ma can sun ga Turofimus mutumin Afisa a birni tare da Bulus suka yi tsammani Bulus ya kawo shi filin haikali.)
30 All the city was also moved and there was a running together of the people, and having laid hold on Paul, they were drawing him out of the temple, and immediately were the doors shut,
Duk birnin ya ruɗe, mutane suka zaburo da gudu daga kowane gefe. Suka kama Bulus, suka ja shi daga haikali, nan da nan aka rurrufe ƙofofi.
31 and they seeking to kill him, a rumor came to the chief captain of the band that all Jerusalem has been thrown into confusion,
Yayinda suke ƙoƙari su kashe shi, sai labari ya kai ga shugaban ƙungiyar sojan Roma cewa birnin Urushalima duk ta hargitse.
32 who, at once, having taken soldiers and centurions, ran down on them, and they having seen the chief captain and the soldiers, left off beating Paul.
Nan da nan ya ɗibi waɗansu hafsoshi da sojoji suka gangara a guje wurin taron. Da masu hargitsin suka ga shugaban ƙungiyar sojan da sojojinsa, sai suka daina dūkan Bulus.
33 Then the chief captain, having come near, took him, and commanded [him] to be bound with two chains, and was inquiring who he may be, and what it is he has been doing,
Shugaban ƙungiyar sojan ya zo ya kama shi ya ba da umarni a daure shi da sarƙoƙi biyu. Sa’an nan ya yi tambaya ko shi wane ne, da kuma abin da ya yi.
34 and some were crying out one thing, and some another, among the multitude, and not being able to know the certainty because of the tumult, he commanded him to be carried into the stronghold,
Waɗansu daga cikin taron suka ɗau kururuwa suna ce abu kaza, waɗansu kuma suna ce abu kaza, da yake shugaban ƙungiyar sojan ya kāsa samun ainihin tushen maganar saboda yawan hayaniyar, sai ya yi umarni a kai Bulus barikin soja.
35 and when he came on the steps, it happened he was carried by the soldiers, because of the violence of the multitude,
Sa’ad da Bulus ya kai bakin matakala, sai da sojoji suka ɗaga shi sama saboda tsananin haukan taron.
36 for the crowd of the people was following after, crying, “Away with him.”
Taron da suka bi suka dinga kururuwa, suna cewa, “A yi da shi!”
37 And Paul being about to be led into the stronghold, says to the chief captain, “Is it permitted to me to say anything to you?” And he said, “Do you know Greek?
Da sojoji suka kai gab da shigar da Bulus cikin bariki, sai ya ce wa shugaban ƙungiyar sojan, “Ko ka yarda in yi magana da kai?” Sai ya amsa ya ce, “Ka iya Girik ne?
38 Are you not, then, the Egyptian who made an uprising before these days, and led the four thousand men of the assassins into the desert?”
Ba kai ba ne mutumin Masar nan da ya haddasa tawaye har ya yi jagorar’yan ta’ada dubu huɗu zuwa hamada a shekarun baya?”
39 And Paul said, “I, indeed, am a man, a Jew, of Tarsus of Cilicia, a citizen of no insignificant city; and I implore you, permit me to speak to the people.”
Bulus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne, daga Tarshish a Silisiya shahararren birnin nan. In ka yarda bari in yi wa mutane magana.”
40 And he having given him leave, Paul having stood on the stairs, beckoned with the hand to the people, and there having been a great silence, he spoke to them in the Hebrew dialect, saying:
Da ya sami izini daga shugaban ƙungiyar sojan, sai Bulus ya tsaya a matakala, ya ɗaga wa taron hannu. Da dukan suka yi shiru, sai ya ce musu da Arameyanci,

< Acts 21 >