< Acts 12 >

1 And about that time, Herod the king put forth his hands to do evil to certain of those of the Assembly,
Kusan a wannan lokaci ne Sarki Hiridus ya kama waɗansu da suke na ikkilisiya, da niyya ya tsananta musu.
2 and he killed James, the brother of John, with the sword,
Ya sa aka kashe Yaƙub, ɗan’uwan Yohanna, da takobi.
3 and having seen that it is pleasing to the Jews, he added to lay hold of Peter also—and they were the days of the Unleavened [Bread]—
Sa’ad da ya ga wannan ya faranta wa Yahudawa rai, sai ya kama Bitrus shi ma. Wannan ya faru kwanakin Bikin Burodi Marar Yisti.
4 whom also having seized, he put in prison, having delivered [him] to four squads of four soldiers to guard him, intending to bring him forth to the people after the Passover.
Bayan ya kama shi, sai ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi gadinsa. Hiridus ya yi niyyar ya yi masa shari’a a gaban mutane bayan Bikin Ƙetarewa.
5 Peter, therefore, indeed, was kept in the prison, and fervent prayer was being made by the Assembly to God for him,
Saboda haka aka tsare Bitrus a kurkuku, amma ikkilisiya ta nace da addu’a ga Allah dominsa.
6 and when Herod was about to bring him forth, the same night was Peter sleeping between two soldiers, having been bound with two chains, guards were also keeping the prison before the door,
A daren da in gari ya waye da Hiridus yake niyyar kawo shi domin a yi masa shari’a, Bitrus yana barci tsakanin sojoji biyu, daure da sarƙoƙi biyu, masu gadi kuma suna bakin ƙofa.
7 and behold, a messenger of the LORD stood by, and a light shone in the buildings, and having struck Peter on the side, he raised him up, saying, “Rise in haste,” and his chains fell from off [his] hands.
Ba zato ba tsammani sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana haske kuma ya haskaka a ɗakin. Ya bugi Bitrus a gefe ya kuma tashe shi ya ce, “Maza, ka tashi!” Sarƙoƙin kuwa suka zube daga hannuwansa.
8 The messenger also said to him, “Gird yourself, and bind on your sandals”; and he did so; and he says to him, “Cast your garment around and follow me”;
Sa’an nan mala’ikan ya ce masa, “Ka sa rigunarka da takalmanka.” Bitrus kuwa ya sa. Mala’ikan ya faɗa masa cewa, “Ka yafa mayafinka ka bi ni.”
9 and having gone forth, he was following him, and he did not know that it is true that which is done through the messenger, and was thinking he saw a vision,
Bitrus ya bi shi suka fita kurkukun, amma bai ma san cewa abin da mala’ikan yake yi tabbatacce ne ba; yana tsammani wahayi yake gani.
10 and having passed through a first ward, and a second, they came to the iron gate that is leading into the city, which opened to them of its own accord, and having gone forth, they went on through one street, and immediately the messenger departed from him.
Suka wuce masu gadi na fari da na biyu, suka kuma isa ƙofar ƙarfe ta shiga birni. Ƙofar kuwa ta buɗe musu da kanta, suka kuma wuce. Sa’ad da suka yi tafiya tsawon wani titi, nan take mala’ikan ya bar shi.
11 And Peter having come to himself, said, “Now I have known of a truth that the LORD sent forth His messenger, and delivered me out of the hand of Herod, and all the expectation of the people of the Jews”;
Sai Bitrus ya dawo hankalinsa ya ce, “Yanzu na sani ba shakka Ubangiji ne ya aiki mala’ikansa yă cece ni daga hannun Hiridus da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
12 also, having considered, he came to the house of Mary, the mother of John, who is surnamed Mark, where there were many thronged together and praying.
Da ya gane haka, sai ya tafi gidan Maryamu uwar Yohanna, wanda ake kuma kira Markus, inda mutane da yawa suka taru suna addu’a.
13 And Peter having knocked at the door of the porch, there came a girl to listen, by name Rhoda,
Bitrus ya ƙwanƙwasa ƙofar waje, sai wata mai aiki a gidan da ake kira Roda ta zo tă ji ko wane ne.
14 and having known the voice of Peter, from the joy she did not open the porch, but having run in, told of the standing of Peter before the porch,
Da ta gane muryar Bitrus, ta cika da murna ta gudu ta koma ba tare da ta buɗe ƙofar ba, sai ta koma a guje ta ce da ƙarfi, “Ga Bitrus a bakin ƙofa!”
15 and they said to her, “You are mad”; and she was confidently affirming [it] to be so, and they said, “It is his messenger”;
Sai suka ce mata, “Kina hauka.” Da ta nace cewa shi ne, sai suka ce, “To, lalle, mala’ikansa ne.”
16 and Peter was continuing knocking, and having opened, they saw him, and were astonished,
Amma Bitrus ya yi ta ƙwanƙwasawa. Da suka buɗe ƙofar suka kuma gan shi, sai suka yi mamaki.
17 and having beckoned to them with the hand to be silent, he declared to them how the LORD brought him out of the prison, and he said, “Declare these things to James and to the brothers”; and having gone forth, he went on to another place.
Bitrus ya yi musu alama da hannunsa su yi shiru sai ya bayyana yadda Ubangiji ya fitar da shi daga kurkuku. Ya ce, “Ku gaya wa Yaƙub da kuma’yan’uwa game da wannan,” sa’an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
18 And day having come, there was not a little stir among the soldiers what then was become of Peter,
Da safe, hargitsin da ya tashi tsakanin sojojin ba ƙarami ba ne, a kan abin da ya sami Bitrus.
19 and Herod having sought for him, and having not found, having examined the guards, commanded [them] to be led away to punishment, and having gone down from Judea to Caesarea, he was abiding [there].
Bayan Hiridus ya neme shi bai same shi ba, sai ya tuhumi masu gadin, ya kuma ba da umarni a kashe su. Sa’an nan Hiridus ya tashi daga Yahudiya ya tafi Kaisariya ya kuma yi’yan kwanaki a can.
20 And Herod was highly displeased with the Tyrians and Sidonians, and with one accord they came to him, and having made a friend of Blastus, who [is] over the bed-chambers of the king, they were asking peace, because of their country being nourished from the king’s;
Yana da rashin jituwa da mutanen Taya da na Sidon; sai suka haɗa kai suka nemi ganawa da shi. Bayan suka sami goyon bayan Bilastus, amintaccen bawan sarki, sai suka nemi salama, domin sun dogara ga ƙasar sarkin don samun abincinsu.
21 and on a set day, Herod having clothed himself in kingly clothing, and having sat down on the judgment seat, was making an oration to them,
A ranar da aka shirya Hiridus, sanye da kayan sarautarsa, ya zauna a gadon sarautarsa ya kuma ya wa mutanen jawabi.
22 and the populace were shouting, “The voice of a god, and not of a man!”
Suka tā da murya suka ce, “Wannan muryar wani allah ne, ba ta mutum ba.”
23 And immediately a messenger of the LORD struck him in return for that he did not give the glory to God, and having been eaten of worms, he expired.
Nan take, domin Hiridus bai yi wa Allah yabo ba, wani mala’ikan Ubangiji ya buge shi, tsutsotsi kuwa suka cinye shi ya kuma mutu.
24 And the word of God grew and multiplied,
Amma maganar Allah ta ci gaba da ƙaruwa ta kuma bazu.
25 and Barnabas and Saul turned back out of Jerusalem, having fulfilled the ministry, having also taken John with [them], who was surnamed Mark.
Sa’ad da Barnabas da Shawulu suka kammala aikinsu, sai suka komo daga Urushalima, tare da Yohanna, wanda ake kira Markus.

< Acts 12 >