< 2 Samuel 1 >

1 And it comes to pass after the death of Saul, that David has returned from striking the Amalekite, and David dwells in Ziklag [for] two days,
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 and it comes to pass, on the third day, that behold, a man has come in out of the camp from Saul, and his garments [are] torn, and earth [is] on his head; and it comes to pass in his coming to David, that he falls to the earth and pays respect.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 And David says to him, “Where do you come from?” And he says to him, “I have escaped out of the camp of Israel.”
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 And David says to him, “What has been the matter? Please declare [it] to me.” And he says, “That the people have fled from the battle, and also a multitude of the people have fallen, and they die; and also Saul and his son Jonathan have died.”
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 And David says to the youth who is declaring [it] to him, “How have you known that Saul and his son Jonathan [are] dead?”
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 And the youth who is declaring [it] to him says, “I happened to meet in Mount Gilboa, and behold, Saul is leaning on his spear; and behold, the chariots and those possessing horses have followed him;
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 and he turns behind him, and sees me, and calls to me, and I say, Here I [am].
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 And he says to me, Who [are] you? And I say to him, I [am] an Amalekite.
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 And he says to me, Please stand over me and put me to death, for the arrow has seized me, for all my soul [is] still in me.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 And I stand over him, and put him to death, for I knew that he does not live after his falling, and I take the crown which [is] on his head, and the bracelet which [is] on his arm, and bring them to my lord here.”
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 And David takes hold on his garments, and tears them, and also all the men who [are] with him,
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 and they mourn, and weep, and fast until the evening, for Saul, and for his son Jonathan, and for the people of YHWH, and for the house of Israel, because they have fallen by the sword.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 And David says to the youth who is declaring [it] to him, “Where [are] you from?” And he says, “I [am] the son of a sojourner, an Amalekite.”
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 And David says to him, “How were you not afraid to put forth your hand to destroy the anointed of YHWH?”
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 And David calls to one of the youths and says, “Draw near—fall on him”; and he strikes him, and he dies;
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 and David says to him, “Your blood [is] on your own head, for your mouth has testified against you, saying, I put to death the anointed of YHWH.”
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 And David laments with this lamentation over Saul, and over his son Jonathan;
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 and he says to teach the sons of Judah “The Bow”; behold, it is written on the Scroll of the Upright:
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 “The beauty of Israel [Is] wounded on your high places; How the mighty have fallen!
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Do not declare [it] in Gath, Do not proclaim the tidings in the streets of Ashkelon, Lest they rejoice—The daughters of the Philistines, Lest they exult—The daughters of the uncircumcised!
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 Mountains of Gilboa! No dew nor rain be on you, And fields of raised-offerings! For there has become loathsome The shield of the mighty, The shield of Saul—without the anointed with oil.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 From the blood of the wounded, From the fat of the mighty, The bow of Jonathan Has not turned backward; And the sword of Saul does not return empty.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saul and Jonathan! They are loved and pleasant in their lives, And in their death they have not been parted. They have been lighter than eagles, They have been mightier than lions!
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 Daughters of Israel! Weep for Saul, Who is clothing you [in] scarlet with delights. Who is lifting up ornaments of gold on your clothing.
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 How the mighty have fallen In the midst of the battle! Jonathan [was] wounded on your high places!
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 I am in distress for you, my brother Jonathan, You were very pleasant to me; Your love was wonderful to me, Above the love of women!
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 How the mighty have fallen, Indeed, the weapons of war perish!”
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”

< 2 Samuel 1 >