< 2 Samuel 21 >

1 And there is a famine in the days of David [for] three years, year after year, and David seeks the face of YHWH, and YHWH says, “[This is] for Saul and for the bloody house, because that he put the Gibeonites to death.”
Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
2 And the king calls for the Gibeonites and says to them—as for the Gibeonites, they [are] not of the sons of Israel, but of the remnant of the Amorite, and the sons of Israel had sworn to them, and Saul seeks to strike them in his zeal for the sons of Israel and Judah—
Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
3 indeed, David says to the Gibeonites, “What do I do for you? And with what do I make atonement? And bless the inheritance of YHWH.”
Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
4 And the Gibeonites say to him, “We have no silver and gold by Saul and by his house, and we have no man to put to death in Israel”; and he says, “What you are saying I do to you.”
Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
5 And they say to the king, “The man who consumed us, and who devised against us—we have been destroyed from stationing ourselves in all the border of Israel—
Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
6 let there be given to us seven men of his sons, and we have hanged them before YHWH, in the height of Saul, the chosen of YHWH.” And the king says, “I give”;
a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
7 and the king has pity on Mephibosheth son of Jonathan, son of Saul, because of the oath of YHWH that [is] between them, between David and Jonathan son of Saul;
Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
8 and the king takes the two sons of Rizpah daughter of Aiah, whom she bore to Saul, Armoni and Mephibosheth, and the five sons of Michal daughter of Saul whom she bore to Adriel son of Barzillai the Meholathite,
Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
9 and gives them into the hand of the Gibeonites, and they hang them in the hill before YHWH; and the seven fall together, and they have been put to death in the days of harvest, in the first [days], the commencement of barley-harvest.
Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
10 And Rizpah daughter of Aiah takes the sackcloth, and stretches it out for herself on the rock, from the commencement of harvest until water has been poured out on them from the heavens, and has not permitted a bird of the heavens to rest on them by day, or the beast of the field by night.
Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
11 And it is declared to David that which Rizpah daughter of Aiah, concubine of Saul, has done,
Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
12 and David goes and takes the bones of Saul, and the bones of his son Jonathan, from the possessors of Jabesh-Gilead, who had stolen them from the broad place of Beth-Shan, where the Philistines hanged them, in the day of the Philistines striking Saul in Gilboa;
sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
13 and he brings up there the bones of Saul, and the bones of his son Jonathan, and they gather the bones of those hanged,
Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
14 and bury the bones of Saul and of his son Jonathan in the land of Benjamin, in Zelah, in the burying-place of his father Kish, and do all that the king commanded, and God accepts the plea for the land afterward.
Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
15 And again the Philistines have war with Israel, and David goes down, and his servants with him, and they fight with the Philistines; and David is weary,
Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
16 and Ishbi-Benob, who [is] among the children of the giant—the weight of his spear [is] three hundred [shekels in] weight of bronze, and he is girded with a new one—speaks of striking David,
Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
17 and Abishai son of Zeruiah gives help to him, and strikes the Philistine, and puts him to death; then the men of David swear to him, saying, “You do not go out with us to battle again, nor quench the lamp of Israel.”
Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
18 And it comes to pass afterward that the battle is again in Gob with the Philistines. Then Sibbechai the Hushathite has struck Saph, who [is] among the children of the giant.
Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
19 And the battle is again in Gob with the Philistines, and Elhanan son of Jaare-Oregim, the Beth-Lehemite, strikes [a brother of] Goliath the Gittite, and the wood of his spear [is] like a weavers’ beam.
Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
20 And the battle is again in Gath, and there is a man of [great] stature, and the fingers of his hands [are] six, and the toes of his feet [are] six—twenty-four in number, and he has also been born to the giant,
Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
21 and he reproaches Israel, and Jonathan son of Shimeah, David’s brother, strikes him;
Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
22 these four have been born to the giant in Gath, and they fall by the hand of David, and by the hand of his servants.
Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.

< 2 Samuel 21 >