< 2 Samuel 2 >
1 And it comes to pass afterward, that David inquires of YHWH, saying, “Do I go up into one of the cities of Judah?” And YHWH says to him, “Go up.” And David says, “To where do I go up?” And He says, “To Hebron.”
Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
2 And David goes up there, and also his two wives, Ahinoam the Jezreelitess, and Abigail wife of Nabal the Carmelite;
Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
3 and David has brought up his men who [are] with him—a man and his household—and they dwell in the cities of Hebron.
Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
4 And the men of Judah come, and anoint David there for king over the house of Judah; and they declare to David, saying, “The men of Jabesh-Gilead [are] they who buried Saul.”
Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
5 And David sends messengers to the men of Jabesh-Gilead and says to them, “Blessed [are] you of YHWH, in that you have done this kindness with your lord, with Saul, that you bury him.
sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
6 And now YHWH does kindness and truth with you, and I also do this good with you because you have done this thing;
Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
7 and now your hands are strong, and be for sons of valor, for your lord Saul [is] dead, and the house of Judah has also anointed me for king over them.”
Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
8 And Abner, son of Ner, head of the host which Saul has, has taken Ish-Bosheth, son of Saul, and causes him to pass over to Mahanaim,
Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
9 and causes him to reign over Gilead, and over the Ashurite, and over Jezreel, and over Ephraim, and over Benjamin, and over Israel—all of it.
Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
10 Ish-Bosheth son of Saul [is] a son of forty years in his reigning over Israel, and he has reigned [for] two years; only the house of Judah has been after David.
Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
11 And the number of the days that David has been king in Hebron, over the house of Judah, is seven years and six months.
Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
12 And Abner son of Ner goes out, and servants of Ish-Bosheth son of Saul, from Mahanaim to Gibeon.
Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
13 And Joab son of Zeruiah, and servants of David, have gone out, and they meet by the pool of Gibeon together, and sit down, these by the pool on this [side], and these by the pool on that [side].
Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
14 And Abner says to Joab, “Now let the youths rise and they play before us”; and Joab says, “Let them rise.”
Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
15 And they rise and pass over, in number twelve of Benjamin, even of Ish-Bosheth son of Saul, and twelve of the servants of David.
Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
16 And they each lay hold on the head of his companion, and his sword [is] in the side of his companion, and they fall together, and [one] calls that place Helkath-Hazzurim, which [is] in Gibeon,
Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
17 and the battle is very hard on that day, and Abner is struck, and the men of Israel, before the servants of David.
Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
18 And there are three sons of Zeruiah there: Joab, and Abishai, and Asahel; and Asahel [is] light on his feet, as one of the roes which [are] in the field,
’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
19 and Asahel pursues after Abner, and has not turned aside to go to the right or to the left, from after Abner.
Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
20 And Abner looks behind him and says, “Are you he—Asahel?” And he says, “I [am].”
Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
21 And Abner says to him, “Turn aside to your right hand or to your left, and seize one of the youths for yourself, and take his armor for yourself”; and Asahel has not been willing to turn aside from after him.
Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
22 And Abner adds again, saying to Asahel, “Turn aside from after me, why do I strike you to the earth? And how do I lift up my face to your brother Joab?”
Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
23 And he refuses to turn aside, and Abner strikes him with the back part of the spear to the fifth [rib], and the spear comes out from behind him, and he falls there, and dies under it; and it comes to pass, everyone who has come to the place where Asahel has fallen and dies—they stand still.
Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
24 And Joab and Abishai pursue after Abner, and the sun has gone in, and they have come to the height of Ammah, which [is] on the front of Giah, the way of the wilderness of Gibeon.
Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
25 And the sons of Benjamin gather themselves together after Abner, and become one troop, and stand on the top of a certain height,
Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
26 and Abner calls to Joab and says, “Does the sword consume forever? Have you not known that it is bitterness in the latter end? And until when do you not say to the people to turn back from after their brothers?”
Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
27 And Joab says, “God lives! For unless you had spoken, surely then from the morning each of the people had gone up from after his brother.”
Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
28 And Joab blows with a horn, and all the people stand still, and no longer pursue after Israel, nor have they added to fight anymore.
Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
29 And Abner and his men have gone through the plain all that night, and pass over the Jordan, and go on [through] all Bithron, and come to Mahanaim.
Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
30 And Joab has turned back from after Abner, and gathers all the people, and there are lacking of the servants of David nineteen men, and Asahel;
Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
31 and the servants of David have struck of Benjamin, even among the men of Abner, three hundred and sixty men—they died.
Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
32 And they lift up Asahel, and bury him in the burying-place of his father, which [is] in Beth-Lehem, and they go all the night—Joab and his men—and [dawn’s light] shines on them in Hebron.
Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.