< 2 Samuel 19 >

1 And it is declared to Joab, “Behold, the king is weeping and mourning for Absalom”;
Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
2 and the salvation on that day becomes mourning to all the people, for the people have heard on that day, saying, “The king has been grieved for his son.”
Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
3 And the people steals away, on that day, to go into the city, as the people steal away, who are ashamed, in their fleeing in battle;
Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
4 and the king has covered his face, indeed, the king cries [with] a loud voice, “My son Absalom! Absalom, my son, my son!”
Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
5 And Joab comes into the house to the king and says, “Today you have put to shame the faces of all your servants, those delivering your life today, and the life of your sons, and of your daughters, and the life of your wives, and the life of your concubines,
Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
6 to love your enemies, and to hate those loving you, for today you have declared that you have no princes and servants, for today I have known that if Absalom [were] alive, and all of us dead today, that then it were right in your eyes.
Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
7 And now, rise, go out and speak to the heart of your servants, for I have sworn by YHWH, that [if] you are not going out—there does not lodge a man with you tonight; and this [is] worse for you than all the evil that has come on you from your youth until now.”
Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
8 And the king rises, and sits in the gate, and they have declared to all the people, saying, “Behold, the king is sitting in the gate”; and all the people come in before the king, and Israel has fled, each to his tents.
Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
9 And it comes to pass, all the people are contending through all the tribes of Israel, saying, “The king delivered us out of the hand of our enemies, indeed, he himself delivered us out of the hand of the Philistines, and now he has fled out of the land because of Absalom,
Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
10 and Absalom whom we anointed over us [is] dead in battle, and now, why are you silent—to bring back the king?”
kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
11 And King David sent to Zadok and to Abiathar the priests, saying, “Speak to [the] elderly of Judah, saying, Why are you last to bring back the king to his house, since the word of all Israel has come to the king, to his house;
Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
12 you [are] my brothers, you [are] my bone and my flesh, and why are you last to bring back the king?
Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
13 And say to Amasa, Are you not my bone and my flesh? Thus God does to me, and thus He adds, if you are not head of the host before me instead of Joab [for] all the days.”
Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
14 And he inclines the heart of all the men of Judah as one man, and they send to the king, “Return, you and all your servants.”
Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
15 And the king turns back, and comes to the Jordan, and Judah has come to Gilgal, to go to meet the king, to bring the king over the Jordan,
Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
16 and Shimei son of Gera, the Benjamite, who [is] from Bahurim, hurries, and comes down with the men of Judah, to meet King David,
Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
17 and one thousand men [are] with him from Benjamin, and Ziba servant of the house of Saul, and his fifteen sons and his twenty servants with him, and they have gone prosperously over the Jordan before the king.
Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
18 And the ferry-boat has passed over to carry over the household of the king, and to do that which [is] good in his eyes, and Shimei son of Gera has fallen before the king in his passing over into the Jordan,
Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
19 and he says to the king, “Do not let my lord impute iniquity to me; neither remember that which your servant did perversely in the day that my lord the king went out from Jerusalem—for the king to set [it] to his heart;
ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
20 for your servant has known that I have sinned; and behold, I have come today, first of all the house of Joseph, to go down to meet my lord the king.”
Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
21 And Abishai son of Zeruiah answers and says, “Is Shimei not put to death for this—because he reviled the anointed of YHWH?”
Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
22 And David says, “And what do I [have to do] with you, O sons of Zeruiah, that today you are for an adversary to me? Is any man put to death in Israel today? For have I not known that today I [am] king over Israel?”
Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
23 And the king says to Shimei, “You do not die”; and the king swears to him.
Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
24 And Mephibosheth son of Saul has come down to meet the king—and he did not prepare his feet, nor did he prepare his upper lip, indeed, he did not wash his garments, even from the day of the going away of the king, until the day that he came in peace—
Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
25 and it comes to pass, when he has come to Jerusalem to meet the king, that the king says to him, “Why did you not go with me, Mephibosheth?”
Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
26 And he says, “My lord, O king, my servant deceived me, for your servant said, I saddle the donkey for myself, and ride on it, and go with the king, for your servant [is] lame;
Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
27 and he utters slander against your servant to my lord the king, and my lord the king [is] as a messenger of God; and do that which is good in your eyes,
Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
28 for all the house of my father have been nothing except men of death before my lord the king, and you set your servant among those eating at your table, and what right do I have anymore—even to cry anymore to the king?”
Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
29 And the king says to him, “Why do you speak anymore of your matters? I have said, You and Ziba—share the field.”
Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
30 And Mephibosheth says to the king, “Indeed, let him take the whole, after that my lord the king has come in peace to his house.”
Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
31 And Barzillai the Gileadite has gone down from Rogelim, and passes over the Jordan with the king, to send him away over the Jordan;
Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
32 and Barzillai [is] very aged, a son of eighty years, and he has sustained the king in his abiding in Mahanaim, for he [is] a very great man;
To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
33 and the king says to Barzillai, “Pass over with me, and I have sustained you in Jerusalem with me.”
Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
34 And Barzillai says to the king, “How many [are] the days of the years of my life, that I go up with the king to Jerusalem?
Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
35 I [am] a son of eighty years today; do I know between good and evil? Does your servant taste that which I am eating, and that which I drink? Do I listen anymore to the voice of male and female singers? And why is your servant for a burden to my lord the king anymore?
Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
36 As a little thing, your servant passes over the Jordan with the king, and why does the king repay me this repayment?
Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
37 Please let your servant turn back again, and I die in my own city, near the burying-place of my father and of my mother—and behold, your servant Chimham, let him pass over with my lord the king, and do to him that which [is] good in your eyes.”
Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
38 And the king says, “Chimham goes over with me, and I do to him that which [is] good in your eyes, indeed, all that you fix on me I do to you.”
Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
39 And all the people pass over the Jordan, and the king has passed over, and the king gives a kiss to Barzillai, and blesses him, and he turns back to his place.
Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
40 And the king passes over to Gilgal, and Chimham has passed over with him, and all the people of Judah, and they bring over the king, and also the half of the people of Israel.
Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
41 And behold, all the men of Israel are coming to the king, and they say to the king, “Why have our brothers, the men of Judah, stolen you—and they bring the king and his household over the Jordan, and all the men of David with him?”
Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
42 And all the men of Judah answer against the men of Israel, “Because the king [is] near to us, and why [is] this [that] you are displeased about this matter? Have we eaten of the king’s [substance] at all? Has he lifted up a gift to us?”
Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
43 And the men of Israel answer the men of Judah, and say, “We have ten parts in the king, and also more than you in David; and why have you lightly esteemed us, that our word has not been first to bring back our king?” And the word of the men of Judah is sharper than the word of the men of Israel.
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.

< 2 Samuel 19 >