< 2 Kings 1 >

1 And Moab transgresses against Israel after the death of Ahab,
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 and Ahaziah falls through the lattice in his upper chamber that [is] in Samaria, and is sick, and sends messengers, and says to them, “Go, inquire of Ba‘al-Zebub god of Ekron if I recover from this sickness.”
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 And a messenger of YHWH has spoken to Elijah the Tishbite, “Rise, go up to meet the messengers of the king of Samaria, and speak to them, Is it because there is not a God in Israel—you are going to inquire of Ba‘al-Zebub god of Ekron?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 And therefore, thus said YHWH: The bed to where you have gone up, you do not come down from it, for you certainly die”; and Elijah goes on.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 And the messengers return to him, and he says to them, “What [is] this—you have turned back!”
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 And they say to him, “A man has come up to meet us and says to us, Go, return to the king who sent you, and you have said to him, Thus said YHWH: Is it because there is not a God in Israel—you are sending to inquire of Ba‘al-Zebub god of Ekron? Therefore, the bed to where you have gone up, you do not come down from it, for you certainly die.”
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 And he says to them, “What [is] the fashion of the man who has come up to meet you, and speaks these words to you?”
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 And they say to him, “A hairy man, and a girdle of skin girt around his loins”; and he says, “He [is] Elijah the Tishbite.”
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 And he sends to him a head of fifty and his fifty, and he goes up to him (and behold, he is sitting on the top of the hill), and he speaks to him, “O man of God, the king has spoken, Come down.”
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 And Elijah answers and speaks to the head of the fifty, “And if I [am] a man of God, fire comes down from the heavens and consumes you and your fifty”; and fire comes down from the heavens and consumes him and his fifty.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 And he turns and sends to him another head of fifty and his fifty, and he answers and speaks to him, “O man of God, thus said the king: Hurry, come down.”
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 And Elijah answers and speaks to them, “If I [am] a man of God, fire comes down from the heavens and consumes you and your fifty”; and fire of God comes down from the heavens and consumes him and his fifty.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 And he turns and sends a third head of fifty and his fifty, and the third head of fifty goes up, and comes in, and bows on his knees before Elijah, and makes supplication to him, and speaks to him, “O man of God, please let my soul and the soul of your servants—these fifty—be precious in your eyes.
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Behold, fire has come down from the heavens and consumes the two heads of the former fifties and their fifties; and now, let my soul be precious in your eyes.”
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 And a messenger of YHWH speaks to Elijah, “Go down with him, do not be afraid of him”; and he rises and goes down with him to the king,
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 and speaks to him, “Thus said YHWH: Because that you have sent messengers to inquire of Ba‘al-Zebub god of Ekron—is it because there is not a God in Israel to inquire of His word? Therefore, the bed to where you have gone up—you do not come down from it, for you certainly die.”
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 And he dies, according to the word of YHWH that Elijah spoke, and Jehoram reigns in his stead, in the second year of Jehoram son of Jehoshaphat king of Judah, for he had no son.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 And the rest of the matters of Ahaziah that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< 2 Kings 1 >