< 2 Kings 7 >

1 And Elisha says, “Hear a word of YHWH! Thus said YHWH: About this time tomorrow, a measure of fine flour [is] at a shekel, and two measures of barley at a shekel, in the Gate of Samaria.”
Sai Elisha ya ce, “Ku ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji ya ce, gobe war haka, za a sayar da mudun gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel ɗaya a ƙofar birnin Samariya.”
2 And the captain whom the king has, by whose hand he has been supported, answers the man of God and says, “Behold, YHWH is making windows in the heavens—will this thing be?” And he says, “Behold, you are seeing it with your eyes, and you do not eat thereof.”
Sai wani hafsa mataimakin sarki ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Sai Elisha ya ce, “Za ka gani da idanunka, zai faru, amma ba za ka ci ba!”
3 And four men have been leprous at the opening of the gate, and they say to one another, “Why are we sitting here until we have died?
To, akwai waɗansu kutare huɗu a ƙofar gari. Suka ce wa junansu, “Don me za mu zauna a nan sai mun mutu?
4 If we have said, We go into the city, then the famine [is] in the city and we have died there; and if we have sat here, then we have died; and now, come and we go down to the camp of Aram; if they keep us alive, we live, and if they put us to death—we have died.”
In muka ce, ‘Za mu shiga cikin birni’ yunwa tana can, za mu kuwa mutu. Idan kuwa muka zauna a nan, za mu mutu. Saboda haka, bari mu ƙetare zuwa sansanin Arameyawa mu miƙa kai. Idan suka bar mu da rai, to; idan kuwa suka kashe mu, shi ke nan.”
5 And they rise in the twilight, to go to the camp of Aram, and they come to the extremity of the camp of Aram, and behold, there is not a man there,
Da yamma sai suka tashi suka tafi sansanin Arameyawa. Yayinda suka shiga tsakiyar sansanin Arameyawa kuwa, sai suka tarar ba kowa a can,
6 seeing YHWH has caused the camp of Aram to hear a noise of chariot and a noise of horse—a noise of great force, and they say to one another, “Behold, the king of Israel has hired against us the kings of the Hittites, and the kings of Egypt, to come against us.”
gama Ubangiji ya sa rundunar Arameyawa suka ji motsin kekunan yaƙi, da motsin dawakai, da na babban rundunar sojoji, saboda haka suka ce wa juna; “Duba, sarkin Isra’ila ya ɗauka hayar sarakuna Hittiyawa da sarakunan Masarawa don su yaƙe mu!”
7 And they rise and flee in the twilight, and forsake their tents, and their horses, and their donkeys—the camp as it [is]—and flee for their life.
Saboda haka suka tashi, suka gudu da yamma, suka bar tentunansu, da dawakansu, da jakunansu. Suka bar sansanin yadda yake, suka gudu don su ceci rayukansu.
8 And these lepers come to the extremity of the camp, and come into one tent, and eat, and drink, and lift up silver, and gold, and garments from there, and go and hide; and they turn back and go into another tent, and lift up from there, and go and hide.
Da kutaren nan suka kai bakin sansanin, sai suka shiga wani tenti, suka ci, suka sha, suka kwashi azurfa, da zinariya, da riguna, suka tafi, suka ɓoye su. Sa’an nan suka koma, suka shiga wani tenti, sai suka kwashi kaya daga ciki, suka kuma ɓoye su.
9 And they say to one another, “We are not doing right this day; it [is] a day of tidings, and we are keeping silent; and we have waited until the morning light, then punishment has found us; and now, come and we go in and declare [it] to the house of the king.”
Sa’an nan suka ce wa juna, “Ba mu yi abin kirki ba. Wannan rana ce ta albishiri amma muka yi shiru; in kuwa mun bari har gari ya waye, to, fa, wata masifa za tă fāɗo mana. Bari mu tafi nan take mu faɗa a fadan sarki.”
10 And they come in, and call to the gatekeeper of the city, and declare for themselves, saying, “We have come to the camp of Aram, and behold, there is no man or sound of man there, but the bound horse, and the bound donkey, and tents as they [are].”
Saboda haka suka je suka kira masu tsaron ƙofar birni, suka ce musu, “Mun je sansanin Arameyawa, ga shi kuwa ba mu iske kowa a can ba, babu ko motsin wani, sai dai dawakai da jakuna a daure, tentunan kuwa suna nan yadda suke.”
11 And he calls the gatekeepers, and they declare [it] to the house of the king within.
Sai matsaran ƙofar suka sanar da labarin a cikin fada.
12 And the king rises by night and says to his servants, “Now let me declare to you that which the Arameans have done to us; they have known that we are famished, and they go out from the camp to be hidden in the field, saying, When they come out from the city, then we catch them alive, and we enter into the city.”
Sai sarki ya tashi da daren nan ya ce wa hafsoshinsa, “Na san abin da Arameyawan suke shiri! Sun san game da yunwar da muke ciki a nan, domin haka sun bar sansaninsu suka shiga jeji suka ɓuya, suna nufin sa’ad da muka fita daga birni, sai su kama mu da rai, sa’an nan su shiga birnin.”
13 And one of his servants answers and says, “Then please let them take five of the horses that are left, that have been left in it—behold, they [are] as all the multitude of Israel who have been left in it; behold, they are as all the multitude of Israel who have been consumed—and we send and see.”
Ɗaya daga cikin fadawan sarki ya ce, “A sa waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka ragu cikin birni, idan ba su tsira ba, za su zama kamar sauran Isra’ilawan da suka riga suka mutu ne. Bari mu aika, mu gani.”
14 And they take two chariot-horses, and the king sends [them] after the camp of Aram, saying, “Go, and see.”
Saboda haka suka zaɓi kekunan yaƙi biyu tare da dawakansu, sarki kuwa ya aike su su bi bayan sojojin Arameyawa. Ya umarci masu tuƙinsu ya ce, “Ku je ku bincika abin da ya faru.”
15 And they go after them to the Jordan, and behold, all the way is full of garments and vessels that the Arameans have cast away in their haste, and the messengers return and declare [it] to the king.
Suka bi sawunsu har Urdun, suka ga tufafi da makamai barjat ko’ina a hanya waɗanda Arameyawa suka zubar yayinda suke gudu. Sai’yan aika suka dawo suka ba wa sarki labari.
16 And the people go out and spoil the camp of Aram, and there is a measure of fine flour at a shekel, and two measures of barley at a shekel, according to the word of YHWH.
Sa’an nan jama’a suka fita suka kwashi ganima a sansanin Arameyawa. Aka kuwa sayar da gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel guda, yadda Ubangiji ya faɗi.
17 And the king has appointed the captain, by whose hand he is supported, over the gate, and the people tread him down in the gate, and he dies, as the man of God spoke, which he spoke in the coming down of the king to him,
Sai ya kasance cewa Sarki ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa’ad da sarki ya tafi wurinsa.
18 indeed, it comes to pass, according to the speaking of the man of God to the king, saying, “Two measures of barley at a shekel, and a measure of fine flour at a shekel are, at this time tomorrow, in the Gate of Samaria”;
Haka kuwa ya kasance kamar yadda mutumin Allah ya ce wa sarki, “Gobe war haka, za a sayar da mudun gari shekel guda, mudun sha’ir biyu ma a shekel guda, a ƙofar Samariya.”
19 and the captain answers the man of God and says, “And behold, YHWH is making windows in the heavens—will this thing be?” And he says, “Behold, you are seeing it with your eyes, and you do not eat thereof”;
Hafsan ya riga ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Mutumin Allah kuwa ya faɗa masa, “Za ka gani da idanunka sai dai ba za ka ci ba!”
20 and it comes to him so, and the people tread him down in the gate, and he dies.
Haka kuwa ya kasance, gama mutane sun tattake shi a hanyar shiga, har ya mutu.

< 2 Kings 7 >