< 2 Kings 13 >
1 In the twenty-third year of Joash son of Ahaziah, king of Judah, Jehoahaz son of Jehu has reigned over Israel in Samaria, seventeen years,
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 and he does evil in the eyes of YHWH, and goes after the sins of Jeroboam son of Nebat, that he caused Israel to sin—he did not turn aside from it,
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 and the anger of YHWH burns against Israel, and He gives them into the hand of Hazael king of Aram, and into the hand of Ben-Hadad son of Hazael, all the days.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 And Jehoahaz appeases the face of YHWH, and YHWH listens to him, for He has seen the oppression of Israel, for the king of Aram has oppressed them—
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 and YHWH gives a savior to Israel, and they go out from under the hand of Aram, and the sons of Israel dwell in their tents as before;
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 only, they have not turned aside from the sins of the house of Jeroboam that he caused Israel to sin, therein they walked, and also, the Asherah has remained in Samaria—
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 for he did not leave to Jehoahaz of the people except fifty horsemen, and ten chariots, and ten thousand footmen, for the king of Aram has destroyed them, and makes them as dust for threshing.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 And the rest of the matters of Jehoahaz, and all that he did, and his might, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 And Jehoahaz lies with his fathers, and they bury him in Samaria, and his son Joash reigns in his stead.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the thirty-seventh year of Joash king of Judah, Jehoash son of Jehoahaz has reigned over Israel in Samaria, sixteen years,
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 and he does evil in the eyes of YHWH, he has not turned aside from all the sins of Jeroboam son of Nebat that he caused Israel to sin, therein he walked.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 And the rest of the matters of Joash, and all that he did, and his might with which he fought with Amaziah king of Judah, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 And Joash lies with his fathers, and Jeroboam has sat on his throne, and Joash is buried in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 And Elisha has been sick with his sickness in which he dies, and Joash king of Israel comes down to him and weeps on his face, and says, “My father, my father, the chariot of Israel, and its horsemen.”
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 And Elisha says to him, “Take bow and arrows”: and he takes bow and arrows for himself.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 And he says to the king of Israel, “Place your hand on the bow”; and he places his hand, and Elisha puts his hands on the hands of the king,
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 and says, “Open the window eastward”; and he opens, and Elisha says, “Shoot,” and he shoots; and he says, “An arrow of salvation from YHWH, and an arrow of salvation against Aram, and you have struck Aram, in Aphek, until consuming.”
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 And he says, “Take the arrows,” and he takes; and he says to the king of Israel, “Strike to the earth”; and he strikes three times, and stays.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 And the man of God is angry against him and says, “By striking five or six times then you had struck Aram until consuming; but now you [only] strike Aram three times.”
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 And Elisha dies, and they bury him, and troops of Moab come into the land at the coming in of the year,
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 and it comes to pass, they are burying a man, and behold, they have seen the troop, and cast the man into the grave of Elisha, and the man goes and comes against the bones of Elisha, and lives, and rises on his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 And Hazael king of Aram has oppressed Israel all the days of Jehoahaz,
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 and YHWH favors them, and pities them, and turns to them for the sake of His covenant with Abraham, Isaac, and Jacob, and has not been willing to destroy them, nor to cast them from His presence as yet.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 And Hazael king of Aram dies, and his son Ben-Hadad reigns in his stead,
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 and Jehoash son of Jehoahaz turns and takes the cities out of the hand of Ben-Hadad son of Hazael that he had taken out of the hand of his father Jehoahaz in war; Joash has struck him three times, and he brings back the cities of Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.