< 2 Chronicles 34 >
1 Josiah [is] a son of eight years in his reigning, and he has reigned thirty-one years in Jerusalem,
Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
2 and he does that which is right in the eyes of YHWH, and walks in the ways of his father David, and has not turned aside [to] the right or left.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
3 And in the eighth year of his reign (and he [is] yet a youth), he has begun to seek for the God of his father David, and in the twelfth year he has begun to cleanse Judah and Jerusalem from the high places, and the Asherim, and the carved images, and the molten images.
A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
4 And they break down the altars of the Ba‘alim before him, and he has cut down the images that [are] on high above them, and the Asherim, and the carved images, and the molten images, he has broken and beaten small, and strews [them] on the surface of the graves of those sacrificing to them,
A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
5 and he has burned the bones of the priests on their altars, and cleanses Judah and Jerusalem,
Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
6 and in the cities of Manasseh, and Ephraim, and Simeon, even to Naphtali, with their tools, all around.
Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
7 And he breaks down the altars and the Asherim, and he has beaten down the carved images very small, and he has cut down all the images in all the land of Israel, and turns back to Jerusalem.
ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
8 And in the eighteenth year of his reign, to purify the land and the house, he has sent Shaphan son of Azaliah, and Maaseiah head of the city, and Joah son of Johaz the remembrancer, to strengthen the house of his God YHWH.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
9 And they come to Hilkiah the high priest, and they give the money that is brought into the house of God, that the Levites, keeping the threshold, have gathered from the hand of Manasseh, and Ephraim, and from all the remnant of Israel, and from all Judah, and Benjamin, and the inhabitants of Jerusalem,
Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
10 and they give [it] into the hand of the workmen, those appointed over the house of YHWH, and they give it [to] the workmen who are working in the house of YHWH, to repair and to strengthen the house;
Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
11 and they give [it] to craftsmen and to builders to buy hewn stones, and wood for couplings and for beams [for] the houses that the kings of Judah had destroyed.
Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
12 And the men are working faithfully in the business, and over them are appointed Jahath and Obadiah, the Levites, of the sons of Merari, and Zechariah and Meshullam, of the sons of the Kohathite, to overlook; and of the Levites, everyone understanding about instruments of song,
Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
13 and over the burden-bearers, and overseers of everyone doing work for every service; and of the Levites [are] scribes, and officers, and gatekeepers.
sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
14 And in their bringing out the money that is brought into the house of YHWH, Hilkiah the priest has found the Scroll of the Law of YHWH by the hand of Moses,
Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
15 and Hilkiah answers and says to Shaphan the scribe, “I have found [the] Scroll of the Law in the house of YHWH”; and Hilkiah gives the scroll to Shaphan,
Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
16 and Shaphan brings in the scroll to the king, and brings the king back word again, saying, “All that has been given into the hand of your servants they are doing,
Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
17 and they pour out the money that is found in the house of YHWH, and give it into the hand of those appointed and into the hands of those doing the work.”
Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
18 And Shaphan the scribe declares [it] to the king, saying, “Hilkiah the priest has given a scroll to me”; and Shaphan reads in it before the king.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
19 And it comes to pass, at the king’s hearing the words of the Law, that he tears his garments,
Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
20 and the king commands Hilkiah, and Ahikam son of Shaphan, and Abdon son of Micah, and Shaphan the scribe, and Asaiah, servant of the king, saying,
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
21 “Go, seek YHWH for me, and for him who is left in Israel and in Judah, concerning the words of the scroll that is found, for great [is] the fury of YHWH that is poured on us, because that our fathers did not keep the word of YHWH to do according to all that is written on this scroll.”
Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
22 And Hilkiah goes, and they of the king, to Huldah the prophetess, wife of Shallum son of Tikvath, son of Hasrah, keeper of the garments, and she is dwelling in Jerusalem in the Second [Quarter], and they speak to her thus.
Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
23 And she says to them, “Thus said YHWH, God of Israel: Say to the man who has sent you to me,
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
24 Thus said YHWH: Behold, I am bringing in calamity on this place and on its inhabitants, all the execrations that are written on the scroll that they read before the king of Judah,
‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
25 because that they have forsaken Me, and make incense to other gods, so as to provoke Me with all the works of their hands, and My fury is poured out on this place, and it is not quenched.
Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
26 And to the king of Judah who is sending you to inquire of YHWH, thus you say to him, Thus said YHWH God of Israel, whose words you have heard:
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
27 Because your heart [is] tender, and you are humbled before God in your hearing His words concerning this place and concerning its inhabitants, and are humbled before Me, and tear your garments, and weep before Me, indeed, I have also heard [you]—a declaration of YHWH.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
28 Behold, I am gathering you to your fathers, and you have been gathered to your graves in peace, and your eyes do not look on all the calamity that I am bringing on this place and on its inhabitants”; and they bring the king back word.
Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
29 And the king sends and gathers all the elderly of Judah and Jerusalem,
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
30 and the king goes up to the house of YHWH, and [to] every man of Judah, and the inhabitants of Jerusalem, and the priests, and the Levites, even all the people, from great even to small, and he reads in their ears all the words of the scroll of the covenant that is found in the house of YHWH.
Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
31 And the king stands on his station, and makes the covenant before YHWH to walk after YHWH, and to keep His commands, and His testimonies, and His statutes, with all his heart and with all his soul, to do the words of the covenant that are written on this scroll.
Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
32 And he presents everyone who is found in Jerusalem and Benjamin, and the inhabitants of Jerusalem do according to the covenant of God, the God of their fathers.
Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
33 And Josiah turns aside all the abominations out of all the lands that the sons of Israel have, and causes everyone who is found in Israel to serve, to serve their God YHWH; all his days they did not turn aside from after YHWH, God of their fathers.
Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.