< 2 Chronicles 32 >
1 After these things and this truth, Sennacherib king of Asshur has come, indeed, he comes to Judah, and encamps against the cities of the bulwarks, and says to break into them himself.
Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
2 And Hezekiah sees that Sennacherib has come, and his face [is] to the battle against Jerusalem,
Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
3 and he takes counsel with his heads and his mighty ones, to stop the waters of the fountains that [are] at the outside of the city—and they help him,
sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
4 and many people are gathered, and they stop all the fountains and the brook that is rushing into the midst of the land, saying, “Why do the kings of Asshur come, and have found much water?”
Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
5 And he strengthens himself, and builds the whole of the wall that is broken, and causes [it] to ascend to the towers, and at the outside of the wall [builds] another, and strengthens Millo [in] the City of David, and makes darts in abundance, and shields.
Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
6 And he puts heads of war over the people, and gathers them to him, to the broad place of a gate of the city, and speaks to their heart, saying,
Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
7 “Be strong and courageous, do not be afraid, nor be cast down from the face of the king of Asshur, and from the face of all the multitude that [is] with him, for with us [are] more than with him.
“Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
8 With him [is] an arm of flesh, but with us [is] our God YHWH to help us and to fight our battles”; and the people are supported by the words of Hezekiah king of Judah.
Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
9 After this Sennacherib king of Asshur has sent his servants to Jerusalem—and he [is] by Lachish, and all his power with him—against Hezekiah king of Judah and against all Judah who [are] in Jerusalem, saying,
Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
10 “Thus said Sennacherib king of Asshur: On what are you trusting and abiding in the bulwark in Jerusalem?
“Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
11 Is Hezekiah not persuading you to give you up to die by famine and by thirst, saying, Our God YHWH delivers us from the hand of the king of Asshur?
Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
12 Has Hezekiah himself not turned aside His high places and His altars, and speaks to Judah and to Jerusalem, saying, You bow yourselves before one altar and you make incense on it?
Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
13 Do you not know what I have done—I and my fathers—to all peoples of the lands? Were the gods of the nations of the lands at all able to deliver their land out of my hand?
“Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
14 Who among all the gods of these nations whom my fathers have devoted to destruction [is] he who has been able to deliver his people out of my hand, that your God is able to deliver you out of my hand?
Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
15 And now, do not let Hezekiah lift you up, nor persuade you thus, nor give credence to him, for no god of any nation and kingdom is able to deliver his people from my hand and from the hand of my fathers: also, surely your God does not deliver you from my hand!”
Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
16 And again his servants have spoken against YHWH God and against His servant Hezekiah,
Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
17 and he has written letters to give reproach to YHWH, God of Israel, and to speak against Him, saying, “As the gods of the nations of the lands that have not delivered their people from my hand, so the God of Hezekiah does not deliver His people from my hand.”
Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
18 And they call with a great voice [in] Jewish against the people of Jerusalem who [are] on the wall, to frighten them and to trouble them, that they may capture the city,
Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
19 and they speak against the God of Jerusalem as against the gods of the peoples of the land—work of the hands of man.
Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
20 And Hezekiah the king prays, and Isaiah son of Amoz the prophet, concerning this, and they cry to the heavens,
Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
21 and YHWH sends a messenger and cuts off every mighty man of valor—both leader and head—in the camp of the king of Asshur, and he turns back with shame of face to his land and enters the house of his god, and those coming out of his bowels have caused him to fall there by the sword.
Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
22 And YHWH saves Hezekiah and the inhabitants of Jerusalem from the hand of Sennacherib king of Asshur and from the hand of all, and He leads them around;
Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
23 and many are bringing in an offering to YHWH, to Jerusalem, and precious things to Hezekiah king of Judah, and he is lifted up before the eyes of all the nations after this.
Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
24 In those days Hezekiah has been sick even to death, and he prays to YHWH, and He speaks to him and has appointed a wonder for him;
A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
25 and Hezekiah has not returned according to the deed [done] to him, for his heart has been lofty, and there is wrath on him and on Judah and Jerusalem;
Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
26 and Hezekiah is humbled for the loftiness of his heart, he and the inhabitants of Jerusalem, and the wrath of YHWH has not come on them in the days of Hezekiah.
Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
27 And Hezekiah has very much riches and honor, and he has made treasures for himself of silver, and of gold, and of precious stone, and of spices, and of shields, and of all [kinds] of desirable vessels,
Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
28 and storehouses for the increase of grain, and new wine, and oil, and stalls for all kinds of livestock, and herds for stalls;
Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
29 and he has made cities for himself, and possessions of flocks and herds in abundance, for God has given very much substance to him.
Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
30 And Hezekiah himself has stopped the upper source of the waters of Gihon, and directs them beneath to the west of the City of David, and Hezekiah prospers in all his work;
Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
31 and so with the ambassadors of the heads of Babylon, those sending to him to inquire of the wonder that has been in the land, God has left him to try him, to know all in his heart.
Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
32 And the rest of the matters of Hezekiah and his kind acts, behold, they are written in the vision of Isaiah son of Amoz the prophet, on the scroll of the kings of Judah and Israel.
Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
33 And Hezekiah lies with his fathers, and they bury him in the highest of the graves of the sons of David, and all Judah and the inhabitants of Jerusalem have done honor to him at his death, and his son Manasseh reigns in his stead.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.