< 2 Chronicles 28 >
1 Ahaz [is] a son of twenty years in his reigning, and he has reigned sixteen years in Jerusalem, and he has not done that which is right in the eyes of YHWH, as his father David,
Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
2 and walks in the ways of the kings of Israel, and has also made molten images for Ba‘alim,
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
3 and has made incense himself in the Valley of the Son of Hinnom, and burns his sons with fire according to the abominations of the nations that YHWH dispossessed from the presence of the sons of Israel,
Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 and sacrifices and makes incense in high places, and on the heights, and under every green tree.
Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
5 And his God YHWH gives him into the hand of the king of Aram, and they strike him, and take captive a great captivity from him, and bring [them] to Damascus, and he has also been given into the hand of the king of Israel, and he strikes him [with] a great striking.
Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
6 And Pekah son of Remaliah slays one hundred and twenty thousand in Judah in one day (the whole [are] sons of valor), because of their forsaking YHWH, God of their fathers.
A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
7 And Zichri, a mighty one of Ephraim, slays Maaseiah son of the king, and Azrikam leader of the house, and Elkanah second to the king.
Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
8 And the sons of Israel take captive of their brothers: two hundred thousand wives, sons, and daughters; and they have also seized much spoil from them, and they bring in the spoil to Samaria.
Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
9 And there has been a prophet of YHWH there (Oded [is] his name), and he goes out before the host that has come to Samaria, and says to them, “Behold, in the fury of YHWH, God of your fathers, against Judah, He has given them into your hand, and you slay among them in rage—it has come to the heavens;
Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
10 and now you are saying to subdue sons of Judah and Jerusalem for menservants and for maidservants for yourselves; but are there not causes of guilt with you before your God YHWH?
Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
11 And now, hear me, and send back the captives whom you have taken captive of your brothers, for the heat of the anger of YHWH [is] on you.”
To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
12 And certain of the heads of the sons of Ephraim (Azariah son of Johanan, Berechiah son of Meshillemoth, and Jehizkiah son of Shallum, and Amasa son of Hadlai), rise up against those coming in from the host,
Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
13 and say to them, “You do not bring in the captives here, for guilt against YHWH [is already] on us, you are saying to add to our sin and to our guilt. For abundant [is] the guilt we have, and the fierceness of anger on Israel.”
Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
14 And the armed men leave the captives and the prey before the heads and all the assembly;
Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
15 and the men who have been expressed by name rise and take hold on the captives, and they have clothed all their naked ones from the spoil, indeed, they clothe them, and shoe them, and cause them to eat and drink, and anoint them, and lead them on donkeys, even every feeble one, and bring them to Jericho, the city of palms, near their brothers, and return to Samaria.
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
16 At that time King Ahaz has sent to the king of Asshur to give help to him;
A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
17 and again the Edomites have come, and strike in Judah, and take captive a captivity.
Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
18 And the Philistines have rushed against the cities of the low country, and of the south of Judah, and capture Beth-Shemesh, and Aijalon, and Gederoth, and Shocho and its villages, and Timnah and its villages, and Gimzo and its villages, and dwell there,
yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
19 for YHWH has humbled Judah because of Ahaz king of Israel, for he made free with Judah, even to commit a trespass against YHWH.
Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
20 And Tilgath-Pilneser king of Asshur comes to him, and does distress him, and has not strengthened him,
Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
21 though Ahaz has taken a portion [out] of the house of YHWH, and [out] of the house of the king, and of the princes, and gives to the king of Asshur, yet it is no help to him.
Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
22 And in the time of his distress—he adds to trespass against YHWH (this King Ahaz),
Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
23 and he sacrifices to the gods of Damascus [which were] those striking him, and says, “Because the gods of the kings of Aram are helping them, I sacrifice to them, and they help me,” and they have been to him to cause him to stumble, and to all Israel.
Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
24 And Ahaz gathers the vessels of the house of God, and cuts in pieces the vessels of the house of God, and shuts the doors of the house of YHWH, and makes altars for himself in every corner in Jerusalem.
Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
25 And in each and every city of Judah he has made high places to make incense to other gods, and provokes YHWH, God of his fathers.
A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
26 And the rest of his matters, and all his ways, the first and the last, behold, they are written on the scroll of the kings of Judah and Israel.
Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 And Ahaz lies with his fathers, and they bury him in the city, in Jerusalem, but have not brought him to the graves of the kings of Israel, and his son Hezekiah reigns in his stead.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.