< 2 Chronicles 22 >

1 And the inhabitants of Jerusalem cause his youngest son Ahaziah to reign in his stead (for the troop had slain all the chiefly that came in with the Arabians to the camp), and Ahaziah son of Jehoram, king of Judah, reigns.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Ahaziah [is] a son of twenty-two years in his reigning, and he has reigned one year in Jerusalem, and the name of his mother [is] Athaliah daughter of Omri;
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 he has also walked in the ways of the house of Ahab, for his mother has been his counselor to do wickedly.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 And he does evil in the eyes of YHWH, like the house of Ahab, for they have been his counselors, after the death of his father, for destruction to him.
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 Also, he has walked in their counsel, and goes with Jehoram son of Ahab, king of Israel, to battle against Hazael king of Aram in Ramoth-Gilead, and they of Ramah strike Joram;
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 and he turns back to be healed in Jezreel because of the wounds with which they had struck him in Ramah, in his fighting with Hazael king of Aram. And Azariah son of Jehoram, king of Judah, has gone down to see Jehoram son of Ahab in Jezreel, for he [is] sick;
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 and to come to Joram has been from God [for] the destruction of Ahaziah; and in his coming he has gone out with Jehoram to Jehu son of Nimshi, whom YHWH anointed to cut off the house of Ahab.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 And it comes to pass, in Jehu’s executing judgment with the house of Ahab, that he finds the heads of Judah and sons of the brothers of Ahaziah, ministers of Ahaziah, and slays them.
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 And he seeks Ahaziah, and they capture him (and he is hiding himself in Samaria), and bring him to Jehu, and put him to death, and bury him, for they said, “He [is] son of Jehoshaphat, who sought YHWH with all his heart”; and there is none of the house of Ahaziah to retain power for the kingdom.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 And Athaliah mother of Ahaziah has seen that her son is dead, and she rises and destroys the whole seed of the kingdom of the house of Judah.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 And Jehoshabeath daughter of the king takes Joash son of Ahaziah, and steals him from the midst of the sons of the king who are put to death, and puts him and his nurse into the inner part of the bed-chambers, and Jehoshabeath daughter of King Jehoram, wife of Jehoiada the priest, because she has been sister of Ahaziah, hides him from the face of Athaliah, and she has not put him to death.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 And he is with them in the house of God hiding himself [for] six years, and Athaliah is reigning over the land.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.

< 2 Chronicles 22 >