< 2 Chronicles 2 >
1 And Solomon says to build a house for the Name of YHWH, and a house for his kingdom,
Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
2 and Solomon numbers seventy thousand men bearing burden, and eighty thousand men hewing in the mountain, and three thousand and six hundred overseers over them.
Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
3 And Solomon sends to Huram king of Tyre, saying, “When you have dealt with my father David, then you send cedars to him to build a house for him to dwell in;
Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
4 behold, I am building a house for the Name of my God YHWH, to sanctify [it] to Him, to make incense before Him, incense of spices, and a continual arrangement, and burnt-offerings at morning and at evening, at Sabbaths, and at new moons, and at appointed times of our God YHWH; this [is] on Israel for all time.
Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
5 And the house that I am building [is] great, for our God [is] greater than all gods;
“Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
6 and who retains strength to build a house for Him, since the heavens, even the heavens of the heavens, do not contain Him? And who [am] I that I build a house for Him, except to make incense before Him?
Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
7 And now, send a wise man to me to work in gold, and in silver, and in bronze, and in iron, and in purple, and crimson, and blue, and knowing to engrave engravings with the wise men who [are] with me in Judah and in Jerusalem, whom my father David prepared;
“Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
8 and send to me cedar-trees, firs, and algums from Lebanon, for I have known that your servants know to cut down trees of Lebanon, and behold, my servants [are] with your servants,
“Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
9 even to prepare trees in abundance for me, for the house that I am building [is] great and wonderful.
don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
10 And behold, I have given to your servants, to hewers, to those cutting the trees, twenty thousand cors of beaten wheat, and twenty thousand cors of barley, and twenty thousand baths of wine, and twenty thousand baths of oil.”
Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
11 And Huram king of Tyre answers in writing, and sends [it] to Solomon: “In the love of YHWH for His people, He has set you [as] king over them.”
Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
12 And Huram says, “Blessed [is] YHWH, God of Israel, who made the heavens and the earth, who has given a wise son to David the king, knowing wisdom and understanding, who builds a house for YHWH, and a house for his kingdom.
Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
13 And now, I have sent a wise man having understanding, of [my] father Huram
“Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
14 (son of a woman of the daughters of Dan, and his father a man of Tyre), knowing to work in gold, and in silver, in bronze, in iron, in stones, and in wood, in purple, in blue, and in fine linen, and in crimson, and to engrave any engraving, and to devise any invention that is given to him, with your wise men, and the wise men of my lord, your father David.
wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
15 And now, the wheat, and the barley, the oil, and the wine, as my lord said, let him send to his servants,
“Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
16 and we cut trees out of Lebanon, according to all your need, and bring them to you—floats by sea, to Joppa, and you take them up to Jerusalem.”
za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
17 And Solomon numbers all the men, the sojourners who [are] in the land of Israel, after the numbering with which his father David numbered them, and they are found [to be] one hundred and fifty thousand and three thousand and six hundred;
Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
18 and he makes from them seventy thousand burden-bearers, and eighty thousand hewers in the mountain, and three thousand and six hundred overseers, to cause the people to work.
Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.