< 1 Samuel 31 >

1 And the Philistines are fighting against Israel, and the men of Israel flee from the face of the Philistines, and fall wounded in Mount Gilboa,
Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
2 and the Philistines follow Saul and his sons, and the Philistines strike Jonathan, and Abinadab, and Malchishua, the sons of Saul.
Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
3 And the battle is hard against Saul, and the archers find him—men with bow—and he is greatly pained by the archers;
Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
4 and Saul says to the bearer of his weapons, “Draw your sword, and pierce me with it, lest they come—these uncircumcised—and have pierced me, and rolled themselves on me”; and the bearer of his weapons has not been willing, for he is greatly afraid, and Saul takes the sword, and falls on it.
Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
5 And the bearer of his weapons sees that Saul [is] dead, and he falls—he also—on his sword, and dies with him;
Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
6 and Saul dies, and three of his sons, and the bearer of his weapons, also all his men, together on that day.
Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
7 And they see—the men of Israel, who [are] beyond the valley, and who [are] beyond the Jordan—that the men of Israel have fled, and that Saul and his sons have died, and they forsake the cities and flee, and Philistines come in, and dwell in them.
Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
8 And it comes to pass on the next day, that the Philistines come to strip the wounded, and they find Saul and his three sons fallen on Mount Gilboa,
Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
9 and they cut off his head, and strip off his weapons, and send [them] into the land of the surrounding Philistines, to proclaim tidings [in] the house of their idols, and [among] the people;
Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
10 and they place his weapons [in] the house of Ashtaroth, and they have fixed his body on the wall of Beth-Shan.
Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
11 And they hear regarding it—the inhabitants of Jabesh-Gilead—that which the Philistines have done to Saul,
Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
12 and all the men of valor arise, and go all the night, and take the body of Saul, and the bodies of his sons, from the wall of Beth-Shan, and come to Jabesh, and burn them there,
Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
13 and they take their bones, and bury [them] under the tamarisk in Jabesh, and fast seven days.
Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.

< 1 Samuel 31 >