< 1 Samuel 17 >

1 And the Philistines gather their camps to battle, and are gathered to Shochoh, which [is] to Judah, and encamp between Shochoh and Azekah, in Ephes-Dammim;
To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
2 and Saul and the men of Israel have been gathered, and encamp by the Valley of Elah, and set in array [for] battle to meet the Philistines.
Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
3 And the Philistines are standing on the mountain on this [side], and Israel is standing on the mountain on that [side], and the valley [is] between them.
Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
4 And a man goes out, the champion from the camps of the Philistines, his name [is] Goliath, from Gath; his height [is] six cubits and a span [[or four cubits and a span]],
Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
5 and a helmet of bronze [is] on his head, and he is clothed [with] a scaled coat of mail, and the weight of the coat of mail [is] five thousand shekels of bronze,
Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
6 and a frontlet of bronze [is] on his feet, and a javelin of bronze between his shoulders,
A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
7 and the wood of his spear [is] like a weavers’ beam, and the flame of his spear [is] six hundred shekels of iron, and the bearer of the buckler is going before him.
Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
8 And he stands and calls to the ranks of Israel, and says to them, “Why do you come out to set in array for battle? [Am] I not the Philistine, and you the servants of Saul? Choose a man for yourselves, and let him come down to me;
Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
9 if he is able to fight with me, and has struck me, then we have been for servants to you; and if I prevail against him, and have struck him, then you have been for servants to us, and have served us.”
In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
10 And the Philistine says, “I have reproached the ranks of Israel this day; give a man to me and we fight together!”
Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
11 And Saul hears—and all Israel—these words of the Philistine, and they are broken down and greatly afraid.
Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
12 And David [is] son of this Ephraimite of Beth-Lehem-Judah, whose name [is] Jesse, and he has eight sons, and the man has become aged among men in the days of Saul;
To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
13 and the three eldest sons of Jesse go, they have gone after Saul to battle; and the name of his three sons who have gone into battle [are] Eliab the firstborn, and his second Abinadab, and the third Shammah.
Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
14 And David is the youngest, and the three eldest have gone after Saul,
Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
15 and David is going and returning from Saul, to feed the flock of his father at Beth-Lehem.
Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
16 And the Philistine draws near, morning and evening, and stations himself [for] forty days.
Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
17 And Jesse says to his son David, “Now take an ephah of this roasted [grain] and these ten loaves for your brothers, and run to the camp to your brothers;
Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
18 and take these ten cuttings of the cheese to the head of the one thousand, and inspect your brothers for welfare, and receive their pledge.”
Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
19 And Saul, and they, and all the men of Israel, [are] in the Valley of Elah, fighting with the Philistines.
Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
20 And David rises early in the morning, and leaves the flock to a keeper, and lifts up, and goes, as Jesse commanded him, and he comes to the path, and to the force which is going out to the rank, and they have shouted for battle;
Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
21 and Israel and the Philistines set in array rank to meet rank.
Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
22 And David lets down the goods from off him on the hand of a keeper of the goods, and runs into the rank, and comes and asks of his brothers of [their] welfare.
Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
23 And he is speaking with them, and behold, a man, the champion, is coming up, his name [is] Goliath the Philistine, from Gath, out of the ranks of the Philistines, and he speaks according to those words, and David hears;
Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
24 and all the men of Israel, when they see the man, flee from his presence, and are greatly afraid.
Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
25 And the men of Israel say, “Have you seen this man who is coming up? For he is coming up to reproach Israel, and it has been—the man who strikes him, the king enriches him with great riches, and he gives his daughter to him, and makes his father’s house free in Israel.”
Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
26 And David speaks to the men who are standing by him, saying, “What is done to the man who strikes this Philistine, and has turned aside reproach from Israel? For who [is] this uncircumcised Philistine that he has reproached the ranks of the living God?”
Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
27 And the people speak to him according to this word, saying, “Thus it is done to the man who strikes him.”
Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
28 And Eliab, his eldest brother, hears when he speaks to the men, and the anger of Eliab burns against David, and he says, “Why [is] this—[that] you have come down? And to whom have you left those few sheep in the wilderness? I have known your pride, and the evil of your heart—for you have come down to see the battle.”
Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
29 And David says, “What have I done now? Is it not a word?”
Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
30 And he turns around from him to another, and says according to this word, and the people return him word as the first word.
Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
31 And the words which David has spoken are heard, and they declare [them] before Saul, and he receives him;
Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
32 and David says to Saul, “Let no man’s heart fall because of him, your servant goes, and has fought with this Philistine.”
Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
33 And Saul says to David, “You are not able to go to this Philistine, to fight with him, for you [are] a youth, and he [has been] a man of war from his youth.”
Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
34 And David says to Saul, “Your servant has been a shepherd among the sheep for his father, and the lion has come—and the bear—and has taken away a sheep out of the drove,
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
35 and I have gone out after him, and struck him, and delivered [it] out of his mouth, and he rises against me, and I have taken hold on his beard, and struck him, and put him to death.
Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
36 Your servant has struck both the lion and the bear, and this uncircumcised Philistine has been as one of them, for he has reproached the ranks of the living God.”
Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
37 And David says, “YHWH, who delivered me out of the paw of the lion, and out of the paw of the bear, He delivers me from the hand of this Philistine.” And Saul says to David, “Go, and YHWH is with you.”
Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
38 And Saul clothes David with his long robe, and has put a helmet of bronze on his head, and clothes him with a coat of mail.
Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
39 And David girded his sword above his long robe, and begins to go, for he has not tried [it]; and David says to Saul, “I am not able to go with these, for I had not tried”; and David turns them aside from off him.
Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
40 And he takes his staff in his hand, and chooses five smooth stones for himself from the brook, and puts them in the shepherds’ vessel that he has, even in the leather pouch, and his sling [is] in his hand, and he draws near to the Philistine.
Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
41 And the Philistine goes on, going and drawing near to David, and the man carrying the buckler [is] before him,
Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
42 and the Philistine looks attentively, and sees David, and despises him, for he was a youth, and ruddy, with a handsome appearance.
Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
43 And the Philistine says to David, “Am I a dog that you are coming to me with sticks?” And the Philistine reviles David by his gods,
Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
44 and the Philistine says to David, “Come to me, and I give your flesh to the bird of the heavens, and to the beast of the field.”
Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
45 And David says to the Philistine, “You are coming to me with sword, and with spear, and with buckler, and I am coming to you in the Name of YHWH of Hosts, God of the ranks of Israel, which you have reproached!
Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
46 This day YHWH shuts you up into my hand—and I have struck you, and turned aside your head from off you, and given the carcass of the camp of the Philistines this day to the bird of the heavens, and to the beast of the earth, and all the earth knows that God is for Israel!
Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
47 And all this assembly knows that YHWH does not save by sword and by spear, for the battle [is] YHWH’s, and He has given you into our hand.”
Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
48 And it has come to pass, that the Philistine has risen, and goes, and draws near to meet David, and David hurries and runs to the rank to meet the Philistine,
Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
49 and David puts forth his hand into the vessel, and takes a stone from there, and slings, and strikes the Philistine on his forehead, and the stone sinks into his forehead, and he falls on his face to the earth.
Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
50 And David is stronger than the Philistine with a sling and with a stone, and strikes the Philistine, and puts him to death, and there is no sword in the hand of David,
Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
51 and David runs and stands over the Philistine, and takes his sword, and draws it out of its sheath, and puts him to death, and cuts off his head with it; and the Philistines see that their hero [is] dead, and flee.
Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
52 And the men of Israel rise—also Judah—and shout, and pursue the Philistines until you enter the valley, and to the gates of Ekron, and the wounded of the Philistines fall in the way of Shaaraim, even to Gath, and to Ekron,
Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
53 and the sons of Israel return from burning after the Philistines, and spoil their camps.
Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
54 And David takes the head of the Philistine, and brings it to Jerusalem, and he has put his weapons in his own tent.
Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
55 And when Saul sees David going out to meet the Philistine, he has said to Abner, head of the host, “Whose son [is] this—the youth, Abner?” And Abner says, “Your soul lives, O king, I have not known.”
Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
56 And the king says, “Ask whose son this [is]—the young man.”
Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
57 And when David turns back from striking the Philistine, then Abner takes him and brings him in before Saul, and the head of the Philistine [is] in his hand;
Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
58 and Saul says to him, “Whose son [are] you, O youth?” And David says, “Son of your servant Jesse, the Beth-Lehemite.”
Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”

< 1 Samuel 17 >