< 1 Samuel 16 >

1 And YHWH says to Samuel, “Until when are you mourning for Saul, and I have rejected him from reigning over Israel? Fill your horn with oil and go, I send you to Jesse the Beth-Lehemite, for I have seen among his sons a king for Myself.”
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
2 And Samuel says, “How do I go? When Saul has heard, then he has slain me.” And YHWH says, “You take a heifer of the herd in your hand, and have said, I have come to sacrifice to YHWH;
Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
3 and you have called for Jesse in the sacrifice, and I cause you to know that which you do, and you have anointed for Me him of whom I speak to you.”
Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
4 And Samuel does that which YHWH has spoken, and comes to Beth-Lehem, and [the] elderly of the city tremble to meet him, and [one] says, “Is your coming peace?”
Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
5 And he says, “Peace; I have come to sacrifice to YHWH, sanctify yourselves, and you have come in with me to the sacrifice”; and he sanctifies Jesse and his sons, and calls them to the sacrifice.
Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
6 And it comes to pass, in their coming in, that he sees Eliab and says, “Surely His anointed [is] here before YHWH.”
Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
7 And YHWH says to Samuel, “Do not look at his appearance, and at the height of his stature, for I have rejected him; for [it is] not as man sees—for man looks at the eyes, and YHWH looks at the heart.”
Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
8 And Jesse calls to Abinadab, and causes him to pass by before Samuel; and he says, “Indeed, YHWH has not fixed on this [one].”
Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
9 And Jesse causes Shammah to pass by, and he says, “Indeed, YHWH has not fixed on this [one].”
Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
10 And Jesse causes seven of his sons to pass by before Samuel, and Samuel says to Jesse, “YHWH has not fixed on these.”
Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
11 And Samuel says to Jesse, “Are the young men finished?” And he says, “Yet the youngest has been left; and behold, he delights himself among the flock”; and Samuel says to Jesse, “Send and take him, for we do not turn around until his coming in here.”
Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
12 And he sends, and brings him in, and he [is] ruddy, with beautiful eyes, and of good appearance; and YHWH says, “Rise, anoint him, for this [is] he.”
Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
13 And Samuel takes the horn of oil, and anoints him in the midst of his brothers, and the Spirit of YHWH prospers over David from that day and onward; and Samuel rises and goes to Ramath.
Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
14 And the Spirit of YHWH turned aside from Saul, and a spirit of sadness from YHWH terrified him;
To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
15 and the servants of Saul say to him, “Now behold, a spirit of sadness [from] God is terrifying you;
Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
16 now let our lord command your servants before you [that] they seek a skillful man playing on a harp, and it has come to pass, in the spirit of sadness [from] God being on you, that he has played with his hand and [it is] well with you.”
Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
17 And Saul says to his servants, “Now provide for me a man playing well—then you have brought [him] to me.”
Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
18 And one of the servants answers and says, “Behold, I have seen a son of Jesse the Beth-Lehemite, skillful in playing, and a mighty, virtuous man, and a man of battle, and intelligent in word, and a man of form, and YHWH [is] with him.”
Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
19 And Saul sends messengers to Jesse and says, “Send to me your son David, who [is] with the flock.”
Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
20 And Jesse takes a donkey, bread, and a bottle of wine, and one kid of the goats, and sends [them] by the hand of his son David to Saul.
Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
21 And David comes to Saul, and stands before him, and he loves him greatly; and he is a bearer of his weapons.
Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
22 And Saul sends to Jesse, saying, “Please let David stand before me, for he has found grace in my eyes.”
Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
23 And it has come to pass, in the spirit of [sadness from] God being on Saul, that David has taken the harp, and played with his hand, and Saul has refreshment and gladness, and the spirit of sadness has turned aside from off him.
Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.

< 1 Samuel 16 >