< 1 Kings 15 >
1 And in the eighteenth year of King Jeroboam son of Nebat, Abijam has reigned over Judah;
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 he has reigned three years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Maachah daughter of Abishalom;
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 and he walks in all the sins of his father that he did before him, and his heart has not been perfect with his God YHWH, as the heart of his father David;
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 but for David’s sake his God YHWH has given to him a lamp in Jerusalem, to raise up his son after him, and to establish Jerusalem,
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 in that David did that which [is] right in the eyes of YHWH, and did not turn aside from all that He commanded him all [the] days of his life—except in the matter of Uriah the Hittite;
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 and there has been war between Rehoboam and Jeroboam all the days of his life.
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 And the rest of the matters of Abijam and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah? And there has been war between Abijam and Jeroboam;
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 and Abijam lies with his fathers, and they bury him in the City of David, and his son Asa reigns in his stead.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 And in the twentieth year of Jeroboam king of Israel, Asa has reigned over Judah,
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 and he has reigned forty-one years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Maachah daughter of Abishalom.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 And Asa does that which [is] right in the eyes of YHWH, like his father David,
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 and removes the whoremongers out of the land, and turns aside all the idols that his fathers made;
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 and also his mother Maachah—he turns her aside from being mistress, in that she made a horrible thing for an Asherah, and Asa cuts down her horrible thing, and burns [it] by the Brook of Kidron;
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 but the high places have not been removed; only, the heart of Asa has been perfect with YHWH [for] all his days,
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 and he brings in the sanctified things of his father, and his own sanctified things, to the house of YHWH: silver, and gold, and vessels.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 And there has been war between Asa and Baasha king of Israel [for] all their days,
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 and Baasha king of Israel goes up against Judah, and builds Ramah, not to permit anyone going out and coming in to Asa king of Judah.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 And Asa takes all the silver and the gold that are left in the treasures of the house of YHWH, and the treasures of the house of the king, and gives them into the hand of his servants, and King Asa sends them to Ben-Hadad, son of Tabrimmon, son of Hezion king of Aram, who is dwelling in Damascus, saying,
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 “A covenant [is] between me and you, between my father and your father; behold, I have sent a reward of silver and gold to you; go, break your covenant with Baasha king of Israel, and he goes up from off me.”
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 And Ben-Hadad listens to King Asa, and sends the heads of the forces that he has against cities of Israel, and strikes Ijon, and Dan, and Abel-Beth-Maachah, and all Chinneroth, besides all the land of Naphtali;
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 and it comes to pass at Baasha’s hearing, that he ceases from building Ramah, and dwells in Tirzah.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 And King Asa has summoned all Judah—there is none exempt—and they lift up the stones of Ramah, and its wood, that Baasha has built, and King Asa builds with them Geba of Benjamin, and Mizpah.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 And the rest of all the matters of Asa, and all his might, and all that he did, and the cities that he built, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah? Only, at the time of his old age he was diseased in his feet;
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 and Asa lies with his fathers, and is buried with his fathers in the city of his father David, and his son Jehoshaphat reigns in his stead.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 And Nadab son of Jeroboam has reigned over Israel, in the second year of Asa king of Judah, and he reigns over Israel two years,
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 and does evil in the eyes of YHWH, and goes in the way of his father, and in his sin that he made Israel to sin.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 And Baasha son of Ahijah, of the house of Issachar, conspires against him, and Baasha strikes him in Gibbethon, which [belonged] to the Philistines—and Nadab and all Israel are laying siege against Gibbethon—
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 indeed, Baasha puts him to death in the third year of Asa king of Judah, and reigns in his stead.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 And it comes to pass, at his reigning, he has struck the whole house of Jeroboam, he has not left any breathing to Jeroboam until his destroying him, according to the word of YHWH, that He spoke by the hand of His servant Ahijah the Shilonite,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 because of the sins of Jeroboam that he sinned, and that he caused Israel to sin, by his provocation with which he provoked YHWH, God of Israel, to anger.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 And the rest of the matters of Nadab and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 And there has been war between Asa and Baasha king of Israel [for] all their days.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 In the third year of Asa king of Judah, Baasha son of Ahijah has reigned over all Israel in Tirzah, twenty-four years,
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 and he does evil in the eyes of YHWH, and walks in the way of Jeroboam, and in his sin that he caused Israel to sin.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.