< 1 Chronicles 27 >

1 And the sons of Israel, after their number, heads of the fathers, and princes of the thousands and of the hundreds, and their officers, those serving the king in any matter of the divisions, that are coming in and going out month by month throughout all months of the year, [are] twenty-four thousand in each division.
Wannan shi ne jerin Isra’ilawa, kawunan iyalai, shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da manyan ma’aikatansu, waɗanda suka yi wa sarki hidima a dukan abin da ya shafi ɓangarorin mayaƙan da suke aiki wata-wata a dukan shekara. Kowane sashe yana da mutane 24,000.
2 Over the first division for the first month [is] Jashobeam son of Zabdiel, and twenty-four thousand [are] on his division;
Wanda yake lura da sashe na fari, na wata na farko, shi ne Yashobeyam ɗan Zabdiyel. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
3 [he was] of the sons of Perez, [and] the head of all princes of the hosts for the first month.
Shi zuriyar Ferez ne kuma babba na dukan shugabannin mayaƙa don wata na farko.
4 And over the division of the second month [is] Dodai the Ahohite, and Mikloth [is] also president of his division, and twenty-four thousand [are] on his division.
Wanda yake lura da sashen don wata na biyu shi ne Dodai mutumin Ahowa; Miklot ne shugaban sashensa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
5 Head of the third host, for the third month, [is] Benaiah son of Jehoiada, the head priest, and twenty-four thousand [are] on his division.
Shugaban mayaƙa na uku, don wata na uku, shi ne Benahiya ɗan Yehohiyada firist. Shi ne babba kuma akwai mutane 24,000 a sashensa.
6 This Benaiah [is] a mighty one of the thirty, and over the thirty, and his son Ammizabad [is in] his division.
Wannan shi ne Benahiya wanda yake ɗaya daga cikin jarumawa Talatin nan kuma shi ne yake babba a cikin Talatin ɗin. Ɗansa Ammizabad ne yake lura da sashensa.
7 The fourth, for the fourth month, [is] Asahel brother of Joab, and his son Zebadiah after him, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na huɗu, don wata na huɗu, shi ne Asahel ɗan’uwan Yowab; ɗansa Zebadiya shi ne magājinsa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
8 The fifth, for the fifth month, [is] the prince Shamhuth the Izrahite, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na biyar don wata na biyar, shi ne Shamhut mutumin Izhar shugaban mayaƙa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
9 The sixth, for the sixth month, [is] Ira son of Ikkesh the Tekoite, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na shida, don wata na shida, shi ne Ira ɗan Ikkesh mutumin Tekowa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
10 The seventh, for the seventh month, [is] Helez the Pelonite, of the sons of Ephraim, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na Bakwai, don wata na bakwai, shi ne Helez mutumin Felon, mutumin Efraim. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
11 The eighth, for the eighth month, [is] Sibbecai the Hushathite, of the Zerahite, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na takwas, don wata na takwas, shi ne Sibbekai mutumin Husha, mutumin Zera. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
12 The ninth, for the ninth month, [is] Abiezer the Antothite, of the Benjamite, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na tara, don wata na tara, shi ne Abiyezer mutumin Anatot, mutumin Benyamin. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
13 The tenth, for the tenth month, [is] Maharai the Netophathite, of the Zerahite, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na goma, don wata na goma, shi ne Maharai mutumin Netofa, mutumin Zera. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
14 Eleventh, for the eleventh month, [is] Benaiah the Pirathonite, of the sons of Ephraim, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na goma sha ɗaya, don wata goma sha ɗaya, shi ne Benahiya mutumin Firaton, mutumin Efraim. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
15 The twelfth, for the twelfth month, [is] Heldai the Netophathite, of Othniel, and twenty-four thousand [are] on his division.
Na goma sha biyu don wata goma sha biyu, shi ne Heldai mutumin Netofa, daga iyalin Otniyel. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
16 And over the tribes of Israel: the leader of the Reubenite [is] Eliezer son of Zichri; of the Simeonite, Shephatiah son of Maachah;
Shugabannin da suke bisa kabilan Isra’ila, bisa mutanen Ruben su ne, Eliyezer ɗan Zikri; bisa mutanen Simeyon shi ne, Shefatiya ɗan Ma’aka
17 of the Levite, Hashabiah son of Kemuel; of the Aaronite, Zadok;
bisa mutanen Lawi shi ne, Hashabiya ɗan Kemuwel; bisa mutanen Haruna shi ne, Zadok;
18 of Judah, Elihu, of the brothers of David; of Issachar, Omri son of Michael;
bisa mutanen Yahuda shi ne, Elihu, ɗan’uwan Dawuda; bisa mutanen Issakar shi ne, Omri ɗan Mika’ilu;
19 of Zebulun, Ishmaiah son of Obadiah; of Naphtali, Jerimoth son of Azriel;
bisa mutanen Zebulun shi ne, Ishmahiya ɗan Obadiya; bisa mutanen Naftali shi ne, Yerimot ɗan Azriyel;
20 of the sons of Ephraim, Hoshea son of Azaziah; of the half of the tribe of Manasseh, Joel son of Pedaiah;
bisa mutanen Efraim shi ne, Hosheya ɗan Azaziya; bisa rabin kabilar Manasse shi ne, Yowel ɗan Fedahiya;
21 of the half of Manasseh in Gilead, Iddo son of Zechariah; of Benjamin, Jaasiel son of Abner; of Dan, Azareel son of Jeroham.
bisa ɗayan rabi kabilar Manasse a Gileyad shi ne, Iddo ɗan Zakariya; bisa mutanen Benyamin shi ne, Ya’asiyel ɗan Abner;
22 These [are the] heads of the tribes of Israel.
bisa mutanen Dan shi ne, Azarel ɗan Yeroham. Waɗannan su ne shugabanni a bisa kabilan Isra’ila.
23 But David has not taken up their number from a son of twenty years and under, for YHWH had said [He would] multiply Israel as the stars of the heavens.
Dawuda bai ƙirga mutanen da suke’yan shekara ashirin ko ƙasa ba, domin Ubangiji ya yi alkawari zai sa Isra’ila su yi yawa kamar taurari a sararin sama.
24 Joab son of Zeruiah has begun to number, but has not finished; and there is wrath against Israel for this, and the number has not gone up in the account of the Chronicles of King David.
Yowab ɗan Zeruhiya ya fara ƙirgan mutanen amma bai gama ba. Hasala ta sauko a kan Isra’ila saboda wannan ƙirge, ba a kuma shigar da adadin a littafin tarihin Sarki Dawuda ba.
25 And Azmaveth son of Adiel [is] over the treasures of the king; and Jonathan son of Uzziah [is] over the treasures in the field, in the cities, and in the villages, and in the towers;
Azmawet ɗan Adiyel shi ne mai lura da ɗakuna ajiyar fada. Yonatan ɗan Uzziya shi ne mai lura da ɗakunan ajiya a yankuna, cikin garuruwa, ƙauyuka da kuma hasumiyoyin tsaro.
26 and Ezri son of Chelub [is] over workmen of the field for the service of the ground;
Ezri ɗan Kelub shi ne mai lura da ma’aikatan gona waɗanda suke nome ƙasar.
27 and Shimei the Ramathite [is] over the vineyards; and Zabdi the Shiphmite [is] over what [is] in the vineyards for the treasures of wine;
Shimeyi mutumin Ramat shi ne mai lura da gonakin inabi. Zabdi mutumin Shifam shi ne mai lura da amfanin gonakin inabi don matsin ruwan inabi.
28 and Ba‘al-Hanan the Gederite [is] over the olives and the sycamores that [are] in the low country; and Joash [is] over the treasures of oil;
Ba’al-Hanan mutumin Geder shi ne mai lura da itatuwan zaitun da na al’ul a gindin tuddan yamma. Yowash shi ne mai lura da tanadin man zaitun.
29 and Shitrai the Sharonite [is] over the herds that are feeding in Sharon; and Shaphat son of Adlai [is] over the herds in the valleys;
Shitrai mutumin Sharon shi ne mai lura da garkuna masu kiwo a Sharon. Shafat ɗan Adlai shi ne mai lura da garkuna a kwari.
30 and Obil the Ishmaelite [is] over the camels; and Jehdeiah the Meronothite [is] over the donkeys;
Obil mutumin Ishmayel shi ne mai lura da raƙuma. Yedehiya mutumin Meronot shi ne mai lura da jakuna.
31 and Jaziz the Hagerite [is] over the flock; all these [are] heads of the substance that King David has.
Yaziz mutumin Hagiri shi ne mai lura da tumaki. Dukan waɗannan shugabanni ne masu lura da mallakar Sarki Dawuda.
32 And Jonathan, David’s uncle, [is] counselor, a man of understanding, [and] he is also a scribe; and Jehiel son of Hachmoni [is] with the sons of the king;
Yonatan, kawun Dawuda, shi ne mashawarci, mutum mai hangen nesa kuma marubuci. Yehiyel ɗan Hakmoni ne ya lura da’ya’yan sarki maza.
33 and Ahithophel [is] counselor to the king; and Hushai the Archite [is] the friend of the king;
Ahitofel shi ne mashawarcin sarki. Hushai mutumin Arkitawa shi ne abokin sarki na kud da kud.
34 and after Ahithophel [is] Jehoiada son of Benaiah, and Abiathar; and the head of the host of the king [is] Joab.
Yehohiyada ɗan Benahiya da Abiyatar ne suka gāji Ahitofel. Yowab shi ne shugaban mayaƙan masarauta.

< 1 Chronicles 27 >