< 1 Chronicles 22 >

1 And David says, “This is the house of YHWH God, and this [is] the altar for burnt-offering for Israel.”
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 And David says to gather the sojourners who [are] in the land of Israel, and appoints hewers to hew hewn-stones to build a house of God.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 And David has prepared iron in abundance for nails for leaves of the gates and for couplings, and bronze in abundance—there is no weighing,
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 and cedar-trees without number, for the Zidonians and the Tyrians brought in cedar-trees in abundance to David.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 And David says, “My son Solomon [is] a youth and tender, and the house to be built for YHWH [is] to be made exceedingly great, for renown and for beauty to all the lands; now let me prepare for it”; and David prepares in abundance before his death.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 And he calls for his son Solomon, and charges him to build a house for YHWH, God of Israel,
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 and David says to his son Solomon, “As for me, it has been with my heart to build a house for the Name of my God YHWH,
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 and the word of YHWH [is] against me, saying, You have shed blood in abundance, and you have made great wars; you do not build a house for My Name, for you have shed much blood to the earth before Me.
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 Behold, a son is born to you; he is a man of rest, and I have given rest to him from all his surrounding enemies, for Solomon is his name, and I give peace and quietness to Israel in his days;
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 he builds a house for My Name, and he is to Me for a son, and I [am] to him for a father, and I have established the throne of his kingdom over Israel for all time.
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Now my son, YHWH is with you, and you have prospered, and have built the house of your God YHWH, as He spoke concerning you.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 Only, may YHWH give wisdom and understanding to you, and charge you concerning Israel, even to keep the Law of your God YHWH;
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 then you prosper, if you observe to do the statutes and the judgments that YHWH charged Moses with concerning Israel; be strong and courageous; do not fear, nor be cast down.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 And behold, in my affliction I have prepared for the house of YHWH one hundred thousand talents of gold, and one million talents of silver; and of bronze and of iron there is no weighing, for it has been in abundance; and I have prepared wood and stones, and you add to them.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 And with you in abundance [are] workmen, hewers and craftsmen of stone and of wood, and every skillful man for every work.
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 Of the gold, of the silver, and of the bronze, and of the iron, there is no number; arise and do, and YHWH is with you.”
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 And David gives charge to all heads of Israel to give help to his son Solomon, [saying],
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 “Is your God YHWH not with you? Indeed, He has given rest to you all around, for He has given the inhabitants of the land into my hand, and the land has been subdued before His people.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Now give your heart and your soul to seek for your God YHWH, and rise and build the sanctuary of YHWH God, to bring in the Ark of the Covenant of YHWH, and the holy vessels of God, to the house that is built for the Name of YHWH.”
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Chronicles 22 >