< Zephaniah 1 >

1 The word of the Lord which came unto Zephanyah the son of Cushi, the son of Gedalyah, the son of Amaryah, the son of Chizkiyah, in the days of Josiah the son of Amon the king of Judah.
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 I will remove, utterly remove all things from off the face of the earth, saith the Lord.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 I will remove man and beast; I will remove the fowls of the heaven, and the fishes of the sea, and the stumbling blocks together with the wicked; and I will cut off man from off the face of the earth, saith the Lord.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 And I will stretch out my hand over Judah, and over all the inhabitants of Jerusalem; and I will cut off the remnant of Ba'al from this place, the name of his ministers with his priests;
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 And those that bow themselves down on the roofs of houses to the host of heaven; and those that bow themselves down that are sworn [to be true] to the Lord and still swear by Malkom;
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 And those that are turned away from following the Lord; and those that have not sought for the Lord, and have not inquired of him.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Be silent in the presence of the Lord Eternal; for nigh is the day of the Lord; for the Lord hath prepared a slaughter, he hath bidden his invited guests.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 And it shall come to pass on the day of the Lord's slaughter, that I will inflict punishment on the princes, and on the king's sons, and on all such as are clothed in garments of a foreign land.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 And I will inflict punishment on all those that leap over the threshold on that day, who fill the house of their master with violence and deceit.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 And it shall come to pass on that day, saith the Lord, that there shall be a loud cry of lamentation from the fish-gate, and a wailing from the second, and [that of] a great breach from the hills.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Wail, ye inhabitants of the mortar-street, for destroyed are all the trading people; cut off are all that were laden with silver.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 And it shall come to pass at that time, that I will search Jerusalem through with lights; and I will inflict punishment on the men that are at rest on their lees, that say in their heart, The Lord will not do good, nor will he do evil.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 And their wealth shall become a booty, and their houses shall be made desolate; and they will build houses, but they shall not inhabit them; and they will plant vineyards, but they shall not drink their wine.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 Nigh is the great day of the Lord, it is nigh, and hasteneth greatly, [there is] the noise of the day of the Lord: bitterly crieth there the mighty man.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 A day of wrath is that day, a day of distress and anxiety, a day of wasting and desolation, a day of darkness and obscurity, a day of clouds and tempestuous gloom,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 A day of the cornet and alarm, against the fenced cities, and against the high battlements.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 And I will bring distress upon men, that they shall walk about like the blind, because against the Lord have they sinned: and their blood shall be poured out like the dust, and their flesh like the dung.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Neither their silver nor their gold shall be able to deliver them on the day of the Lord's wrath; through the fire of whose zeal the whole land shall be devoured; for destruction, yea, quite sudden, will he prepare for all the inhabitants of the land.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Zephaniah 1 >