< Zechariah 9 >
1 The prophecy of the word of the Lord concerning the land of Chadrach, and Damascus his resting-place; for unto the Lord [will look] the eye of men, and [that of] all the tribes of Israel;
Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
2 And also concerning Chamath that is bordering thereon, Tyre, and Zidon, though it be very wise.
da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
3 And though Tyre have built herself a strong-hold, and heaped up silver as the dust, and fine gold as the mire of the streets:
Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
4 Behold, the Lord will drive her out, and he will strike down her power into the sea; and she herself shall be devoured with fire.
Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
5 Ashkelon shall see it, and fear; Gazzah also, and tremble greatly: and 'Ekron, for her trust will be made ashamed: and the king shall vanish from Gazzah, and Ashkelon shall not be inhabited.
Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
6 And aliens shall dwell in Ashdod, and I will cut off the pride of the Philistines.
Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
7 And I will remove their bloody [-sacrifices] out of their mouth, and their abominations from between their teeth; and their land also shall be left for our God, and it shall be as a prince's [dwelling] in Judah, and 'Ekron shall be like Jebusi.
Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
8 And I will encamp about my house against armies, against those that pass to and fro, and there shall not pass over them any more an oppressor; for now do I look [on them] with my eyes.
Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
9 Be greatly glad, O daughter of Zion; shout, O daughter of Jerusalem! behold, thy King will come unto thee, righteous and victorious is he, lowly, and riding upon an ass, and upon a colt the foal of a she-ass.
Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
10 And I will cut off chariots from Ephraim, and horses from Jerusalem, and there shall be cut off the battle-bow, and he shall speak peace unto the nations; and his dominion shall be from sea to sea, and from the river to the ends of the earth.
Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
11 As for thee also, because of the blood of thy covenant, do I send forth thy prisoners out of the pit wherein there is no water.
Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
12 Return you to the strong-hold, ye hopeful prisoners: even today do I declare, that I will recompense twofold [good] unto thee.
Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
13 For I do bend Judah for me, grasp Ephraim [as] a bow; and I will stir up thy sons, O Zion, against thy sons, O Javan, and I will render thee as the sword of a mighty man.
Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
14 And the Lord will appear over them, and then will go forth like the lightning his arrow: and the Lord Eternal will blow on the cornet, and he will go along in the tempests of the south.
Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
15 The Lord of hosts will be a shield over them; and they shall devour [the prey], and subdue the sling-stones; and they shall drink, make a noise as one [drunken with] wine; and they shall be filled like the offering-bowls, like the corners of the altar.
Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
16 And the Lord their God will save them on that day as the flock of his people; for [like] the stones of a crown, will they elevate themselves over his land.
Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
17 For how great will be [that generation's] happiness, and how great its beauty! corn shall make the young men sing joyfully, and new wine the virgins.
Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.