< Zechariah 14 >

1 Behold, a day is coming unto the Lord, when thy spoil shall be divided in the midst of thee.
Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2 And I will assemble all the nations against Jerusalem to battle; and the city shall be captured, and the houses plundered, and the women ravished; and half of the city shall go forth into exile, and the residue of the people shall not be cut off from the city.
Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3 Then will the Lord go forth, and fight against these nations, as on the day when he fought on the day of battle.
Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
4 And his feet will stand on that day upon the mount of Olives, which is before Jerusalem on the east, and the mount of Olives shall be split in twain in its middle eastward and westward, making a very great valley; and half of the mount shall remove northward, and half of it southward.
A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
5 And ye shall flee [from] the valley of my mountains; for the valley of the mountains shall reach unto Azal; and ye shall flee, just as ye fled from before the earthquake in the days of 'Uzziyah the king of Judah: and then will come the Lord my God, and all the saints with thee.
Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6 And it shall come to pass on that day, that there shall be no light, but fleeting light and thick darkness;
A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
7 But it shall be one particular day which shall indeed be known as the Lord's, neither day nor night; but it shall come to pass, that at evening-time there shall be light.
Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8 And it shall happen on that day, that living waters shall go out from Jerusalem, the half of them toward the eastern sea, and the other half of them toward the western sea: in summer and in winter shall it be so.
A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
9 And the Lord will be king over all the earth: on that day shall the Lord be [acknowledged] one, and his name be one.
Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10 All the land shall be changed as it were into a plain from Geba' to Rimmon to the south of Jerusalem; and she herself shall be elevated, and be inhabited on her former site, from the gate of Benjamin unto the place of the first gate, up to the corner gate, and from the tower of Chananel unto the king's wine-presses.
Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
11 And men shall dwell in it, and no destruction shall any more take place; but Jerusalem shall be inhabited in safety.
Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12 And this shall be the plague wherewith the Lord will afflict all the people that shall have come to battle against Jerusalem: The flesh of every one shall consume away while he standeth upon his feet, and his eyes shall consume away in their holes, and the tongue of every one shall consume away in his mouth.
Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
13 And it shall come to pass on that day, that a great confusion from the Lord shall be among them: and they shall lay hold every one on the hand of his neighbor, and his hand shall rise up against the hand of his neighbor.
A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
14 And also Judah will have to fight against Jerusalem: and there shall be gathered together the wealth of all the nations round about, gold, and silver, and garments, in great abundance.
Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
15 And thus shall be the plague of the horses, of the mules, of the camels, and of the asses, and of all the beasts that will be in these camps, just like this plague.
Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16 And it shall come to pass, that every one that is left out of all the nations who will have come against Jerusalem, yea, these shall go up year by year to bow down before the King, the Lord of hosts, and to celebrate the feast of tabernacles.
Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
17 And it shall happen, that whoso will not come up out of the families of the earth unto Jerusalem to bow down before the King, the Lord of hosts, —even upon these there shall be no rain.
In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
18 And if the family of Egypt go not up, and come not, then shall not [any rain fall] upon them also: this shall be the plague, wherewith the Lord will afflict the nations that will not come up to celebrate the feast of tabernacles.
In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
19 This shall be the punishment of Egypt, and the punishment of all the nations that will not come up to celebrate the feast of tabernacles.
Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20 On that day shall [every thing], even to the bells of the horses, be holy unto the Lord; and the pots in the Lord's house shall be like the bowls before the altar.
A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
21 And every pot in Jerusalem and in Judah shall be holy unto the Lord of hosts; and all those that sacrifice will come and take some of them, and seethe therein: and on that day there shall be no more any trader in the house of the Lord of host.
Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.

< Zechariah 14 >