< Zechariah 11 >

1 Open thy doors, O Lebanon, and the fire shall eat on thy cedars.
Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
2 Wail, fir-tree; for fallen is the cedar; those that were mighty are despoiled: wail, O ye oaks of Bashan; for the impervious forest is come down.
Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
3 [There is] the noise of the wailing of the shepherds; for wasted is their glory: [there is] the noise of the roaring of young lions; for wasted is the pride of the Jordan.
Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
4 Thus hath said the Lord my God, Feed the flocks [that are destined for] the slaughter;
Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
5 Whom their buyers slay, and hold themselves guiltless; and whose sellers say, Blessed be the Lord, for I am rich: and none of whose shepherds have pity on them.
Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
6 For I will no more have pity on the inhabitants of the land, saith the Lord: but, lo, I will deliver the men every one into the hand of his neighbor, and into the hand of his king: and they shall beat down the land, and I will not deliver out of their hand.
Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
7 And I had fed the flocks [that were destined for] the slaughter, —indeed, the poorest of the flocks; and I had taken unto me two staves; the one I called Mildness [[No'am]], and the other I called Concord [[Choblim]]: and I fed the flocks.
Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
8 And I removed the three shepherds in one month; and my soul was tired of them, and also their soul abhorred me.
Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
9 Then said I, I will not feed you: what is dying may die; and what is to be lost may be lost; and those that are left may eat every one the flesh of the other.
na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
10 And I took my staff, namely, Mildness, and cut it to pieces, to annul my covenant which I had made with all the tribes.
Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
11 And when it was annulled on that day, then knew they well, truly the poorest of the flocks that waited for me, that it was the word of the Lord.
An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
12 And I said unto them, If it be good in your eyes, give me my reward; and if not, forbear. So they weighed out as my reward thirty pieces of silver.
Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
13 And the Lord said unto me, Cast it unto the treasurer, the precious price which I am prized at by them. And I took the thirty pieces of silver, and cast them in the house of the Lord unto the treasurer.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
14 Then I cut in pieces my second staff, namely, Concord, to annul the brotherhood between Judah and Israel.
Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
15 And the Lord said unto me, Take unto thee yet the instruments of a foolish shepherd.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
16 For, lo, I raise up a shepherd in the land, who will not think of those that are lost, nor seek for that which is gone astray, nor heal that which hath [a limb] broken; who will not care for that which hath stood still; but who will eat the flesh of the fat, and devour all even to their claws.
Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
17 Woe to the worthless shepherd that leaveth the flock! the sword shall be upon his arm, and upon his right eye: his arm shall utterly wither, and his right eye shall be completely blinded.
“Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”

< Zechariah 11 >