< Psalms 90 >

1 BOOK FOURTH: “A prayer of Moses the man of God.” Lord, a place of refuge hast thou been unto us in all generations.
Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
2 Before yet the mountains were brought forth, or thou hadst ever produced the earth and the world, even from everlasting to everlasting, thou art God.
Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
3 Thou turnest man to contrition, and sayest, Return ye children of men.
Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
4 For a thousand years are in thy eyes but as the yesterday when it is past, and as a watch in the night.
Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
5 Thou carriest them away as with a flood; they are as a sleep: in the morning [they grow] like the grass which changeth.
Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
6 In the morning it blossometh, and is changed: in the evening it is mowed off, and withereth.
ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
7 For [thus] are we consumed by thy anger, and by thy fury are we terrified.
An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
8 Thou hast set our iniquities before thee, our concealed sins before the light of thy countenance.
Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
9 For all our days are passed away in thy wrath: we consume our years like a word that is spoken.
Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
10 The days of our years in this life are seventy years; and if by uncommon vigor they be eighty, yet is their greatness trouble and mishap; for it soon hasteneth off, and we fly away.
Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
11 Who knoweth the strength of thy anger, and thy wrath which is like the fear of thee?
Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
12 Let us then know how to number our days, that we may obtain a heart endowed with wisdom.
Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
13 Return, O Lord, how long yet? and bethink thee concerning thy servants.
Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
14 O satisfy us in the morning with thy kindness, that we may be glad and rejoice throughout all our days.
Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
15 Cause us to rejoice as many days as those wherein thou hast afflicted us, the years wherein we have seen unhappiness.
Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
16 Let thy act be visible on thy servants, and thy majesty over their children.
Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
17 And may the beauty of the Lord our God be upon us; and the work of our hands do thou firmly establish upon us: yea, the work of our hands—firmly establish thou it.
Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.

< Psalms 90 >