< Psalms 89 >

1 “A Maskil of Ethan the Ezrachite.” The kindnesses of the Lord will I for ever sing: from generation to generation will I make known thy faithfulness with my mouth.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 For I have said, To eternity will kindness be built up: the heavens—yea, in these wilt thou establish thy faithfulness.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 “I have made a covenant with my elect, I have sworn unto David my servant,
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 Unto eternity will I establish thy seed, and I will build up thy throne, from generation to generation.” (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 And the heavens praise thy wonder, O Lord: also thy faithfulness in the assembly of holy ones.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 For who in the sky can be compared unto the Lord? who can be likened unto the Lord among the sons of the mighty?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 God is greatly terrific in the secret council of the holy ones and fear-inspiring over all that are about him.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 O Lord God of hosts, who is powerful, like thee, Eternal! and thy faithfulness is round about thee.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Thou rulest over the pride of the sea: when its waves are lifted up, thou assuagest them.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Thou didst crush Rahab as one that is slain: with thy strong arm didst thou scatter thy enemies.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Thine are the heavens, also thine is the earth: as for the world and what filleth it, thou hast founded them.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 The north and the south—these hast thou created: Tabor and Chermon shall rejoice in thy name.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Thine is the powerful arm, with might: strong is thy hand, and exalted is thy right hand.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Righteousness and justice are the prop of thy throne: kindness and truth precede thy presence.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Happy is the people that know the cornet's sound: O Lord, in the light of thy countenance will they ever walk firmly.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 In thy name will they be glad all the day, and in thy righteousness will they be exalted.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 For thou art the glory of their strength; and through thy favor will our horn be exalted.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 For of the Lord is our shield; and of the Holy One of Israel is our king.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Then spokest thou in a vision to thy pious [servant], and saidst, “I have bestowed help to one that is mighty; I have exalted a youth out of the people;
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 I have found David my servant; with my holy oil have I anointed him;
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 With whom my hand shall be firmly established; also my arm shall strengthen him;
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 The enemy shall not exact from him like a lender: and the son of injustice shall not afflict him:
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 And I will beat down before his face his assailants, and those that hate him will I plague.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 But my faithfulness and my kindness shall be with him: and through my name shall his horn be exalted.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 And I will place on the sea his hand, and on the rivers his right hand.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 He will call unto me, Thou art my father, my God, and the rock of my salvation.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Also I will appoint my first-born, the highest among the kings of the earth.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 For evermore will I keep for him my kindness, and my covenant shall stand faithfully with him.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 And I appoint for ever his seed, and his throne as the days of heaven.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 If his children forsake my law, and walk not in my ordinances;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 If they profane my statutes, and keep not my commandments:
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Then will I visit with the rod their transgressions, and with plagues their iniquity.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Nevertheless my kindness will I not make utterly void from him, and I will not act falsely against my faithfulness.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 I will not profane my covenant, and what is gone out of my lips will I not alter.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 One thing have I sworn by my holiness, that I will not lie unto David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 His seed shall endure for ever, and his throne shall be like the sun before me.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Like the moon shall it be firmly established for ever, and as this faithful witness in the sky.” (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 And yet thou hast east off and despised, thou hast become wroth with thy anointed.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Thou hast made void the covenant of thy servant: thou hast profaned, down to the ground, his crown.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Thou hast broken down all his fences: thou hast brought his strong-holds to terror.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 All that pass by the way plunder him: he is become a reproach to his neighbors.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Thou hast raised up the right hand of his assailants: thou hast caused all his enemies to rejoice.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Thou hast also turned the edge of his sword, and hast not let him stand erect in the battle.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Thou hast made his brilliancy cease; and his throne hast thou thrown down to the ground.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Thou hast shortened the days of his youth: thou hast enshrouded him with shame. (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 How long, Lord, wilt thou hide thyself, continually? how long shall thy fury burn like fire?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Remember [what] I am, what my duration is [here], for what nothingness thou hast created all sons of men!
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 What man is there that can live, and shall not see death? that can deliver his soul from the power of the nether word? (Selah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Where are thy former kindnesses, O Lord, which thou hast sworn unto David by thy truth?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Remember, Lord, the disgrace of thy servants; that I bear in my bosom the [burden] of all the many nations;
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 That thy enemies have defied, O Lord; that they have defied the footsteps of thy anointed.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Blessed be the Lord for evermore. Amen, and Amen.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Psalms 89 >