< Psalms 82 >
1 “A psalm of Assaph.” God standeth in the congregation of God, in the midst of judges doth he judge.
Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
2 How long will ye judge unjustly, and treat with favor the face of the wicked? (Selah)
“Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
3 Judge uprightly the poor and fatherless: do justice to the afflicted and indigent.
Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
4 Release the poor and needy: deliver them out of the power of the wicked.
Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
5 They know not, nor will they understand; in darkness do they walk on: all the foundations of the earth are moved.
“Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
6 I have indeed said, Ye are gods; and children of the most High are all of you.
“Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
7 But verily like men shall ye die, and like one of the princes shall ye fall.
Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
8 Arise, O God, judge the earth; for thou wilt possess all the nations.
Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.