< Psalms 78 >

1 “A Maskil of Assaph.” Give ear, O my people, to my instruction: incline thy ear to the words of my mouth.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 I will open with a parable my mouth: I will utter riddles out of ancient times;
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Which we have heard and know, and which our fathers have related unto us.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 We will not conceal them from their children, relating to the latest generation the praises of the Lord, and his strength, and his wonderful deeds which he hath done.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Yea, he established a testimony in Jacob, and instituted a law in Israel, which he commanded our fathers, that they should make them known to their children:
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 In order that the latest generation might know them, even the children that are to be born; that they may arise and relate them to their children;
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 That they may place in God their hope, and not forget the doings of God, but observe his commandments;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 And that they may not be like their fathers, a stubborn and rebellious generation; a generation that had not directed their heart firmly, and whose spirit was not faithful to God.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 The children of Ephraim, like well-armed archers, that turn round on the day of battle,
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Kept not the covenant of God, and in his law they refused to walk;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 And they forgot his deeds, as also his wonders, which he had permitted them to see.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 In the presence of their fathers did he do wonders, in the land of Egypt, in the fields of Zo'an.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 He divided the sea, and caused them to pass through; and he made the waters stand upright as a wall.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 And he led them with the cloud by day, and all the night with a light of fire.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 He split rocks in the wilderness, and gave them drink as out of the mighty deep.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 And he brought forth running streams out of the rock, and caused water to run down like rivers.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 But they repeated to sin yet more against him, rebelling against the Most High in the desert.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 And they tempted God in their heart, by asking food for their desire.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Yea, they spoke against God: they said, Will God be able to set in order a table in the wilderness?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Behold, he smote the rock, so that waters gushed out, and streams overflowed: shall he also be able to give bread? or can he provide flesh for his people?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Therefore, when the Lord heard this, he became wroth: and a fire was kindled against Jacob, and anger also ascended against Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Because they had not believed in God, and had not trusted in his salvation.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Then he ordained the skies from above, and the doors of heaven he opened;
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 And he let rain down upon them manna to eat, and the corn of heaven gave he unto them.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Angels' bread did man eat: he sent them provision to satisfaction.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 He caused an east wind to pass along the heavens; and he led forth by his strength the south wind.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 And he let rain upon them flesh [as plentiful] as the dust, and winged birds like the sand of the sea;
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 And he let them fall in the midst of their camp, round about their habitations.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 And they ate, and were greatly satisfied, and what they longed for he brought unto them.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 They were not estranged from their longing, yet was their food in their mouth:
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 When the wrath of God ascended against them, and he slew some of the fattest of them, and the young men of Israel did he strike down.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 With all this they sinned again, and believed not in his wonders.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Therefore he caused their days to come to an end in nought, and their years in dread.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 When he slew them, then did they seek him, and they returned and inquired earnestly after God.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 And they remembered that God was their rock, and the most high God their redeemer.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Nevertheless they prayed insincerely to him with their mouth, and with their tongue they lied unto him.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 For their heart was not firm with him, and they were not faithful in his covenant.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 But he, being merciful, forgave the iniquity, and destroyed [them] not: yea, many a time turned he his anger away, and did not awaken all his fury.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 And he remembered that they are but flesh, a spirit that passeth away, and returneth not again.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 How oft did they rebel against him in the wilderness, grieve him in the desert!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Yea, they once more tempted God, and set limits to the Holy One of Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 They remembered not his hand, the day when he ransomed them from the adversary;
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 When he displayed in Egypt his signs, and his wonderful tokens in the fields of Zo'an.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 And he changed their rivers into blood; and their running streams, that they could not drink [of them].
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 He sent out among them various wild beasts, which devoured them; and frogs, which destroyed them.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 And he gave unto the cricket their products, and their labor unto the locust.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 He slew with hail their vines, and their sycamore-trees with ice-bolts.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 And he surrendered to the hail their cattle, and their herds to the lightning's flashes.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 He let loose against them the fierceness of his anger, wrath and indignation, and distress, a host of angels of misfortune.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 He leveled a path for his anger; he withheld not from death their soul, and their life he surrendered to the pestilence;
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 And he smote all the first-born in Egypt; the first of their strength in the tents of Ham;
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 But he caused his own people to depart like flocks, and guided them like a drove in the wilderness.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 And he led them in safety, so that they felt no dread; but the sea covered over their enemies.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 And he brought them to his holy territory, even to this mount, which his right hand had acquired.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 And he drove out from before them nations, and divided them by the measuring-line as an inheritance, and he caused to dwell in their tents the tribes of Israel.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Yet they tempted and rebelled against the most high God, and his testimonies they kept not;
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 But swerved aside, and dealt unfaithfully like their fathers; they turned about like a deceitful bow.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 And they provoked him to anger with their high-places, and with their graven images they moved him to jealousy.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 God heard this, and he became wroth, and felt greatly disgusted with Israel;
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 And he cast off the dwelling at Shiloh, the tabernacle where he had dwelt among men;
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 And he gave up his strength unto captivity, and his glory into the adversary's hand.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 And he surrendered his people unto the sword; and with his inheritance was he wroth.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 His young men the fire devoured; and his virgins were not demanded in marriage.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 His priests fell by the sword; and his widows did not weep.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Then awoke the Lord as one that sleepeth, like a mighty man that shouteth by reason of wine.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 And he smote his enemies backward: a perpetual disgrace on them.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Yet was he disgusted with the tent of Joseph, and of the tribe of Ephraim he made not choice;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 But he chose the tribe of Judah, the mount Zion which he loved.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 And he built like high [mountains] his sanctuary, like the earth which he hath founded for ever.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 And he made choice of David his servant, and took him from the sheep-folds:
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 From following the ewes with young he brought him, to feed Jacob his people, and Israel his inheritance.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 And he fed them according to the integrity of his heart; and by the skilfulness of his hands did he lead them.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Psalms 78 >