< Psalms 60 >

1 “To the chief musician upon Shushan'eduth, a Michtham of David, to teach, When he fought with Aram-naharayim, and with Aram-zobah, and Joab returned, and smote of Edom in the Salt Valley twelve thousand [men].” O God, thou hast cast us off, thou hast made a breach in us, thou hast been displeased: restore now unto us [thy favor].
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Thou hast caused the earth to quake; thou hast split it: heal her breaches; for she is moved.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Thou hast caused thy people to see hard things: thou hast made us to drink the wine of confusion.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 Thou hast given to those that fear thee a banner, to elevate themselves, because of the truth. (Selah)
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 In order that thy beloved may be delivered: help with thy right hand, and answer me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 God hath spoken in his holiness: I will exult, I will divide Shechem, and the valley of Succoth will I measure out.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Mine is Gil'ad, and mine is Menasseh; Ephraim also is the strong-hold of my head; of Judah are my chiefs;
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab is my washpot; upon Edom will I cast my shoe: Philistia, triumph thou but over me.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Who will bring me into the fortified city? who will lead me as far as Edom?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Behold, it is thou, O God, who hast cast us off; and thou, O God, goest not forth with our armies.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Give us help against the assailant; for vain is the help of man.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 Through God shall we do valiantly: and he it is that will tread down our assailants.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< Psalms 60 >