< Psalms 59 >

1 “To the chief musician, Al-tashcheth, by David, a Michtham, when Saul sent, and they watched the house to put him to death.” Deliver me from my enemies, O my God: defend me from them that rise up against me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Deliver me from the workers of wickedness, and from men of blood do thou save me.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 For, lo, they lie in wait for my soul, the mighty are gathered in troops against me: not for my transgression, nor for my sin, O Lord.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Without guilt [in me] they run and make themselves ready: awake, [come] toward me, and behold.
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 And thou, O Lord God of hosts, the God of Israel, awake to punish all the nations: be not gracious to any treacherous wicked one. (Selah)
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 They will return at evening; they will howl like dogs, and go round about the city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Behold, they sputter with their mouth: swords are in their lips; for who, [say they, ] doth hear?
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 But thou, O Lord, wilt laugh at theme: thou wilt hold in derision all the nations.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Because of [the enemy's] strength will I wait upon thee; for God is my defence.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 The God who showeth me kindness will go before me: God will let me see [my desire] upon those who regard me with envy.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 Slay them not, that my people may not forget: drive them about by thy power; and bring them down, thou our shield, O Lord.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 The sin of their mouth is the word of their lips: let them be caught through their pride, because of the cursing and lying which they relate.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Make an end in fury, make an end [of them], that they my be no more, and let them know that God ruleth in Jacob, as far as the ends of the earth. (Selah)
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 And they will return in the evening; they will howl like dogs, and go round about the city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 They will indeed roam about after something to eat, if they be not satisfied, so that they can be at rest.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 But I will truly sing of thy strength; yea, I will sing joyfully in the morning of thy kindness; for thou hast been a defence unto me and a refuge on the day when I was distressed.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 Unto thee, O my strength, will I sing; for God is my defence, the God of my kindness.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Psalms 59 >