< Psalms 37 >
1 “Of David.” Do not fret thyself because of the evil-doers, neither be thou envious against the workers of iniquity.
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 For like the grass they shall soon be mowed down, and like the green herb shall they wither.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Trust in the Lord, and do good; dwell in the land, and feed [thyself] with truthfulness.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 And delight thyself in the Lord, and he will give thee the wishes of thy heart.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Commit thy way unto the Lord, and trust in him: and he will accomplish it.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 And he will bring forth as the light thy righteousness, and the justice of thy [cause] as the noonday.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Be silent before the Lord, and wait patiently for him: fret not thyself because of him who prospereth in his way, because of the man who practices wicked devices.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Cease from anger, and forsake wrath: fret not thyself in any wise to do evil.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 For evil-doers shall be cut off; but those that wait upon the Lord, these—shall truly inherit the land.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 For yet but for a little while, and the wicked shall be no more: yea, thou wilt look carefully at his place, and he shall not be there.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 But the meek shall inherit the land, and shall delight themselves because of the abundance of peace.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 The wicked purposeth evil against the just, and gnasheth against him with his teeth.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 The Lord will laugh at him; for he seeth that his day is coming.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 The wicked have drawn out the sword, and have bent their bow, to cause the poor and needy to fall, and to slaughter such as are of an upright course [of life].
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 [But] their sword shall enter into their own heart, and their bows shall be broken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Better is the little that the righteous hath, than the great riches of many wicked.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 For the arms of the wicked shall be broken: but the upholder of the righteous is the Lord.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 The Lord regardeth the days of the upright: and their inheritance shall endure for ever.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 They shall not be made ashamed in the time of unhappiness; and in the days of famine shall they be satisfied.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 But the wicked shall perish, and the enemies of the Lord shall be as the beauty of the meadow: they pass away; in smoke they pass away.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 The wicked borroweth, and repayeth not; but the righteous is beneficent, and giveth.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 For those blessed of him shall inherit the land; and those cursed of him shall be cut off.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 By the Lord are the steps of the righteous man established; and he findeth pleasure in his course [of life].
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Though he fall, he shall not be utterly cast down; for the Lord upholdeth his hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 I have been young, and I am also grown old: yet have I never seen the righteous forsaken, nor his seed seeking for bread.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 He is all the time beneficent, and lendeth: and his seed will be for a blessing.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Depart from evil, and do good; and dwell for evermore.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 For the Lord loveth justice, and never forsaketh his pious servants: they are for ever preserved; but the seed of the wicked will be cut off.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 The righteous shall inherit the land, and dwell for ever therein.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 The mouth of the righteous uttereth wisdom, and his tongue speaketh what is just.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 The law of his God is in his heart: none of his steps shall slip.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 The wicked looketh out for the righteous, and seeketh to slay him.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 The Lord will not leave him in his hand, and will not condemn him when he is judged.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Wait on the Lord, and keep his way, and he will exalt thee to inherit the land: when the wicked are cut off, shalt thou look on.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 I have seen the wicked terrible in power, and striking root like a green tree in its native soil.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Yet he passed away, and, lo, he was no more: and I sought him, but he could not be found.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Observe the perfect man, and behold the upright; for there is a [happy] future for the man of peace.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 But the transgressors are destroyed together: the future of the wicked is cut off.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 And the salvation of the righteous is from the Lord: he is their strong-hold in the time of distress.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 And the Lord helpeth them, and delivereth them; he will deliver them from the wicked, and save them; because they have put their trust in him.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.